Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya amince da biyan alawus-alawus na wata daya ga dubban masu aikin sa kai da ke yaki da Boko Haram.
Zulum ya bayyana haka ne a ranar Litinin a lokacin da ya karbi bakwancin shugabannin bangarori daban-daban na masu aikin sa kai da masu tsaftar muhalli da ke aiki a cikin birnin Maiduguri da kuma karamar hukumar Jere a jihar.
Gwamnan ya hada da ma’aikatan tsaftar muhalli da ke aikin tsaftace al’ummomin da ‘yan tada kayar baya suka lalata kafin a sake gina su da kuma masu tsafta da ke aiki a cibiyoyin gwamnati da hukumomi.
Ya kuma ce,”A madadin daukacin al’ummar jihar Borno, ina mika sakon godiyarmu a gare ku. Muna godiya na har abada ga dukan sadaukarwar da ku ke yi. Tun daga karfe 6:00 na safe, da yawa daga cikinku kuna kan titunan mu ku na shara”. Inji Zulum.
Kungiyoyin sun hada da Civilian Joint Task Force (CJTF) da kuma mafarautar jihar.