fidelitybank

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Date:

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa game da rasuwar fitaccen mai taimakon jama’a, Alhaji Aminu Dantata wanda ya rasu a ranar Juma’a.

Hakan na kunshe ne a cikin sakon ta’aziyyar mai dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Hon. Eseme Eyiboh, ranar Lahadi.

Akpabio ya bayyana marigayi Dantata a matsayin mutum mai kishin zuciya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen taimakawa marasa galihu.

“Marigayi Aminu Dantata ya nuna kauna ga bil’adama ta yadda ya jajirce wajen ganin halin da talakawa da mabukata suke ciki, ayyukan taimakon sa ya kasance wanda ba za a manta da shi ba a tarihin kasarmu,” in ji Akpabio.

Ya kara da cewa ya san Dantata a matsayin mutum mai hazaka kuma mai kyauta wanda ya yi arzikinsa ta hanyar kwazo da sana’a.

Ya kara da cewa irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar Kano da Arewacin Najeriya da ma kasa baki daya na da dimbin yawa.

Shugaban majalisar dattawan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Dantata, jama’a da gwamnatin jihar Kano, da ‘yan kasuwar Najeriya.

Ya bayyana marigayi dan kasuwan a matsayin ginshiki, wanda ya cancancta, kuma mutumin da ba za a iya mantawa da shi ba a Najeriya.

“A gaskiya Marigayi Dantata cibiya ce ta kan sa, ya cancanci a yi koyi da shi kuma ya dawwama,” in ji shi.

“A madadin iyalai na, da ‘yan mazaba, da Majalisar Dattawa, da kuma daukacin Majalisar Dokoki ta kasa, ina mika ta’aziyyata ga iyalan Dantata tare da addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya ba shi Aljannar Firdausi,” sanarwar ta karkare.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp