Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya tabbatarwa da iyalan marigayi ya Hanifa Abubakar, cewa zai mara baya wajen ganin an bi hakkin Hanifa.
Sanata Kwankwaso, wanda ya bayar da wannan tabbacin a ranar Lahadi, yayin da ya ziyarci iyalanta, domin yi musu ta’aziya.
A na dai zargin Abdulmalik Tanko da hallaka Hanifa ‘yar shekara 5, bayan yayi garkuwa da ita, tare inda ya binne ta a makarantar sa ta Nobles Kids Academy da ke Kwanar Dakata, a karamar hukumar Nasarwawa a jihar Kano.