fidelitybank

Buhari ya rantsar da sabon Minista

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da sabon minista da wanda ya wakilci jihar Taraba, Malam Muazu Sambo.

An gudanar da taron ne jim kadan gabanin bude taron kwamitin tsaro na kasa a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Juma’a.

Sambo ya maye gurbin tsohon Ministan wutar lantarki, Mamman Sale, daga Taraba, an mayar da shi ma’aikatar ayyuka da gidaje a matsayin karamin ministan ayyuka da gidaje.

A halin yanzu dai shugaba Buhari ya na jagorantar taron majalisar tsaro na kasa a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Wadanda su ka halarci taron na tsaro sun hada da mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da ministocin harkokin ‘yan sanda da shari’a da kuma na tsaro, harkokin cikin gida da na kasashen waje.

Sauran sun hada da hafsoshin tsaro, mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya; Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Usman Baba; Babban Darakta Janar na Ma’aikatar Harkokin Waje, Yusuf Bichi da kuma Darakta Janar na NIA, Abubakar Rufa’i.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp