fidelitybank

TAJBANK ya zama gwarzon bankin musulunci na shekara

Date:

Bankin da baya ta’ammali da kuɗin ruwa, TAJBank ya zama shine gwarzon bankin musulunci na shekara.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa TAJBank ya lashe kyautar ne a wani bikin bada kyaututtuka na shekara ga bankuna da sauran ma’aikatun harkar kuɗaɗe na BAFI 2021, da jairdar BusinessDay ta gudanar.

Wannan kyautar ta zo ne watanni biyu bayan da bankin ya lashe kyautar gwarzon shekara da jaridar Leadership ta gudanar.

Mahukunta a kamfanin BusinessDay, a wata sanarwar da su ka fitar, sun ce TAJBank ya lashe kyautar ne sakamakon ƙir-ƙire na harkar banki da ya ke yi da kuma yadda ya ke daɗaɗawa abokan hulɗarsa.

Sanarwar ta ce” TAJBank ya bada mamaki a harkar banki bayan kafa shi a 2019.

“Yadda bankin ya kawo sauyi mai kyau da kuma ƙirƙire-ƙirƙire da wasu tsare-tsare ma zamani da kuma yadda ya ke bunƙasa harkar kuɗaɗe da daɗaɗawa abokan hulɗa, ya bada mamaki ƙwarai,”

Mahukuntan kuma sun yi hasashen cewa nan da 2021 zuwa 2026, harkar bankin musulunci za ta samu bunƙasa da kaso 15 cikin ɗari.

Jaridar ta kara da cewa in dai TAJBank ya sami lasisin yin harkar banki na ƙasa, to zai ƙara bunƙasa da kashi 65 cikin 100.

Da ya ke bayani bayan bada lambar girman, shugaban TAJBank, Hamid Joɗa ya nuna cewa nasarar ta nuna cewa lallai bankin ma kan hanyarsa ta ƙoƙarin bunƙasa harkar banki maras ruwa a Nijeriya.

 

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaƙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ƙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp