fidelitybank

Jack Dorsey zai sauka daga mukamin shugaban kamfanin Twitter

Date:

A na sa ran shugaban Kamfanin Twitter, Jack Dorsey zai sauka daga mukaminsa na zartarwa a kamfanin.

Wakilin majiyar CNBC, David Faber, ya rawaito cewa, hannun jarin Twitter ya hauro sama da kashi 11 biyo bayan wallafa labarin.

A halin yanzu Dorsey ya na aiki a matsayin shugaba na Twitter da Square, kamfanin biyan kuɗi na dijital. Wani mai ruwa da tsaki na Twitter, Elliott ya nemi ya maye gurbin Jack Dorsey a matsayin Shugaba a shekarar 2020 kafin kamfanin saka hannun jari ya cimma yarjejeniya da mahukuntan kamfanin.

Wanda ya kafa Elliott kuma hamshakin attajirin nan, Paul Singer ya tambayi ko Dorsey ya kamata ya tafiyar da kamfanonin biyu, ya na mai kira a gare shi da ya sauka a matsayin Shugaba na daya daga cikinsu.

Sai dai ba a san wanda zai gaji Dorsey ba, duk da cewa, idan ya sauka, shugaba na gaba dole ne ya cimma muradan manufofin na Twitter. Kamfanin ya ce a farkon wannan shekarar yana da burin samun kudi miliyan 315 a kullum a karshen shekarar 2023, kuma a kalla ninkin kudaden shigar da yake samu na shekara a waccan shekarar.

A watan Yuni ne gwamnatin Najeriyar ta dakatar da ayyukan Twitter a kasar nan, inda ta ce ta na barazana ga kamfanoninta.

A baya dai shafin Twitter ya goge wani sako da shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya wallafa game da ‘yan Kudu maso Ggabas wanda da dama daga cikin ‘yan Najeriya ke ganin bai dace ba.

Sai dai a ranar Lahadin da ta gabata, karamin Ministan Neja Delta, Festus Keyamo, ya ce kamfanin Twitter ya amince da cika dukkan sharuddan da gwamnatin Najeriya ta gindaya mata a matsayin wani sharadi na dage haramcin.

 

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp