fidelitybank

Ta’addanci: Sojoji sun ragargaji yaran Turji a Sokoto

Date:

Rundunar Sojojin kasar nan sun kashe ’yan ta’adda da dama a musayar wuta da su ka yi da yaran dan bindigar nan, Bello Turji a Jihar Sokoto.

Yaran na Bello Turji sun gamu da ajalinsu ne a kauyukan Katanga da Satiru, bayan Babban da Kwamanda (GOC) na Runduna ta 8 ta Sojin kasa ta Najeriya ya jagoranci sojoji su ka shiga har kauyukan sun yi musu kofar rago a ranar Alhamis.

Aminiya ta rawaito cewa, wani dan sa-kai da ke tare da sojoji a lokacin harin ya ce, “A akalla motoci 20 ne su ka yi wa wurin dirar mikiya, mun dauki awanni mu na musayar wuta da su; In takaita maka bayani, har sai da jirgin yaki ya kawo dauki mu ka fatattake su suka ja baya. Zuwa yanzu da wuya a iya tantance yawan wadanda mu ka kashe, amma ba a kashe mana ko mutum daya ba. Mun samu nasara”.

Bayanan da Aminiya ta samu sun nuna cewa baya kauyukan Katanga da Satiru na hanun Turji da yaransa, suna cin karensu babu babbaka.

Wani mazaunin garin, Isa ya shaida cewa, a lokacin da a ke ba-ta-kashin, sun ga dandazon ’yan bindiga na zuwa wurin, domin marawa ’yan uwansu baya.

“Amma bayanan da muka samu sun nuna sun kwashi kashinsu a hannun sojoji; Yanzu haka GOC da dakarunsa na bin daji suna share ’yan bindigar a maboyansu”. A cewarsa.

Wata majiyar soji ta ce GOC din ya lashi takobi cewa ba zai kowa gida ba sai sun gama fatattakar ’yan bindiga daga yankin Gabashin Jihar Sakkwato.

“Jajirtacce ne kuma ba ya son duk abin da zai kawo nakasu, shi da kan shi ya ke jagorantar sojoji a daji,” inji majiyar.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp