fidelitybank

Ta’addanci: Sojoji sun ragargaji yaran Turji a Sokoto

Date:

Rundunar Sojojin kasar nan sun kashe ’yan ta’adda da dama a musayar wuta da su ka yi da yaran dan bindigar nan, Bello Turji a Jihar Sokoto.

Yaran na Bello Turji sun gamu da ajalinsu ne a kauyukan Katanga da Satiru, bayan Babban da Kwamanda (GOC) na Runduna ta 8 ta Sojin kasa ta Najeriya ya jagoranci sojoji su ka shiga har kauyukan sun yi musu kofar rago a ranar Alhamis.

Aminiya ta rawaito cewa, wani dan sa-kai da ke tare da sojoji a lokacin harin ya ce, “A akalla motoci 20 ne su ka yi wa wurin dirar mikiya, mun dauki awanni mu na musayar wuta da su; In takaita maka bayani, har sai da jirgin yaki ya kawo dauki mu ka fatattake su suka ja baya. Zuwa yanzu da wuya a iya tantance yawan wadanda mu ka kashe, amma ba a kashe mana ko mutum daya ba. Mun samu nasara”.

Bayanan da Aminiya ta samu sun nuna cewa baya kauyukan Katanga da Satiru na hanun Turji da yaransa, suna cin karensu babu babbaka.

Wani mazaunin garin, Isa ya shaida cewa, a lokacin da a ke ba-ta-kashin, sun ga dandazon ’yan bindiga na zuwa wurin, domin marawa ’yan uwansu baya.

“Amma bayanan da muka samu sun nuna sun kwashi kashinsu a hannun sojoji; Yanzu haka GOC da dakarunsa na bin daji suna share ’yan bindigar a maboyansu”. A cewarsa.

Wata majiyar soji ta ce GOC din ya lashi takobi cewa ba zai kowa gida ba sai sun gama fatattakar ’yan bindiga daga yankin Gabashin Jihar Sakkwato.

“Jajirtacce ne kuma ba ya son duk abin da zai kawo nakasu, shi da kan shi ya ke jagorantar sojoji a daji,” inji majiyar.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp