Rundunar Sojojin kasar nan sun kashe ’yan ta’adda da dama a musayar wuta da su ka yi da yaran dan bindigar nan, Bello Turji a Jihar Sokoto.
Yaran na Bello Turji sun gamu da ajalinsu ne a kauyukan Katanga da Satiru, bayan Babban da Kwamanda (GOC) na Runduna ta 8 ta Sojin kasa ta Najeriya ya jagoranci sojoji su ka shiga har kauyukan sun yi musu kofar rago a ranar Alhamis.
Aminiya ta rawaito cewa, wani dan sa-kai da ke tare da sojoji a lokacin harin ya ce, “A akalla motoci 20 ne su ka yi wa wurin dirar mikiya, mun dauki awanni mu na musayar wuta da su; In takaita maka bayani, har sai da jirgin yaki ya kawo dauki mu ka fatattake su suka ja baya. Zuwa yanzu da wuya a iya tantance yawan wadanda mu ka kashe, amma ba a kashe mana ko mutum daya ba. Mun samu nasara”.
Bayanan da Aminiya ta samu sun nuna cewa baya kauyukan Katanga da Satiru na hanun Turji da yaransa, suna cin karensu babu babbaka.
Wani mazaunin garin, Isa ya shaida cewa, a lokacin da a ke ba-ta-kashin, sun ga dandazon ’yan bindiga na zuwa wurin, domin marawa ’yan uwansu baya.
“Amma bayanan da muka samu sun nuna sun kwashi kashinsu a hannun sojoji; Yanzu haka GOC da dakarunsa na bin daji suna share ’yan bindigar a maboyansu”. A cewarsa.
Wata majiyar soji ta ce GOC din ya lashi takobi cewa ba zai kowa gida ba sai sun gama fatattakar ’yan bindiga daga yankin Gabashin Jihar Sakkwato.
“Jajirtacce ne kuma ba ya son duk abin da zai kawo nakasu, shi da kan shi ya ke jagorantar sojoji a daji,” inji majiyar.