fidelitybank

Rasha ta gargadi Amurka a kan kasar Ukraine

Date:

Shugaban kasar Russia, Vladimir Putin ya gargadi takwaransa na Amurka, Joe Biden, cewa kakaba sabbin takunkumii kan Ukraine na iya haifar da wargajewar dangantakar da ke a tsakani.

A wata wayar tarho da ya yi da yammacin ranar Alhamis, shugaban na Rasha ya ce, irin wannan takunkumin zai zama “kuskure babba”.

A halin da ake ciki a yanzu, Biden ya shaidawa Putin cewa Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri kan duk wani hari da a ka kaiwa Ukraine.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, wannan kiran da Rasha ta nema, shi ne karo na biyu da su ka yi irin wannan tattaunawa a wannan watan kuma ya dauki kusan sa’a guda.

Wannan dai shi ne wani yunkuri na baya-bayan nan na kwantar da tarzoma a kan iyakar Gabashin Ukraine da Rasha, inda jami’an Ukraine su ka ce an aike da sojojin Rasha fiye da 100,000.

Wannan ci gaban ya haifar da damuwa a kasashen Yammacin duniya, inda Amurka ta yi wa Putin barazanar kakabawa Putin takunkumi “kamar wanda bai taba gani ba” mudin idan Ukraine ta fuskanci hari.

Sai dai Rasha ta musanta cewa ta na shirin mamaye kasar, kuma ta ce sojojin na can ne domin yin atisaye, kuma ta ce ta na da damar motsa sojojinta cikin walwala a kasarta.

Duk da cewa bangarorin biyu sun yi musayar kashedi a yayin ganawar, mai ba da shawara kan harkokin wajen Rasha, Yuri Ushakov, ya shaida wa manema labarai jim kadan bayan ganawar Mr Putin ya ji dadin tattaunawar. Ya kara da cewa, hakan ya haifar da “ dankwan alaka mai kyau” domin tattaunawa a nan gaba.

Wani babban jami’in Amurka, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ganawar ta su ya kasance mai mahimmanci kuma mai ma’ana.

“Shugaba Biden ya sake nanata cewa, gagarumin ci gaba a cikin wadannan tattaunawa na iya faruwa ne kawai a cikin yanayi na tabarbarewar,” in ji Sakatariyar yada labaran Fadar White House Jen Psaki.

Ta kara da cewa “Ya bayyana karara cewa, Amurka da kawayenta da abokan huldarta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine.”

 

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaƙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ƙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp