fidelitybank

Rasha ta gargadi Amurka a kan kasar Ukraine

Date:

Shugaban kasar Russia, Vladimir Putin ya gargadi takwaransa na Amurka, Joe Biden, cewa kakaba sabbin takunkumii kan Ukraine na iya haifar da wargajewar dangantakar da ke a tsakani.

A wata wayar tarho da ya yi da yammacin ranar Alhamis, shugaban na Rasha ya ce, irin wannan takunkumin zai zama “kuskure babba”.

A halin da ake ciki a yanzu, Biden ya shaidawa Putin cewa Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri kan duk wani hari da a ka kaiwa Ukraine.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, wannan kiran da Rasha ta nema, shi ne karo na biyu da su ka yi irin wannan tattaunawa a wannan watan kuma ya dauki kusan sa’a guda.

Wannan dai shi ne wani yunkuri na baya-bayan nan na kwantar da tarzoma a kan iyakar Gabashin Ukraine da Rasha, inda jami’an Ukraine su ka ce an aike da sojojin Rasha fiye da 100,000.

Wannan ci gaban ya haifar da damuwa a kasashen Yammacin duniya, inda Amurka ta yi wa Putin barazanar kakabawa Putin takunkumi “kamar wanda bai taba gani ba” mudin idan Ukraine ta fuskanci hari.

Sai dai Rasha ta musanta cewa ta na shirin mamaye kasar, kuma ta ce sojojin na can ne domin yin atisaye, kuma ta ce ta na da damar motsa sojojinta cikin walwala a kasarta.

Duk da cewa bangarorin biyu sun yi musayar kashedi a yayin ganawar, mai ba da shawara kan harkokin wajen Rasha, Yuri Ushakov, ya shaida wa manema labarai jim kadan bayan ganawar Mr Putin ya ji dadin tattaunawar. Ya kara da cewa, hakan ya haifar da “ dankwan alaka mai kyau” domin tattaunawa a nan gaba.

Wani babban jami’in Amurka, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ganawar ta su ya kasance mai mahimmanci kuma mai ma’ana.

“Shugaba Biden ya sake nanata cewa, gagarumin ci gaba a cikin wadannan tattaunawa na iya faruwa ne kawai a cikin yanayi na tabarbarewar,” in ji Sakatariyar yada labaran Fadar White House Jen Psaki.

Ta kara da cewa “Ya bayyana karara cewa, Amurka da kawayenta da abokan huldarta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine.”

 

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp