fidelitybank

Rana ta 11: Sojoji sun harbe masu zanga-zanga a Sudan

Date:

Jami’an tsaron kasar Sudan sun harbe mutane hudu a wani samame da a ka yi a fadin kasar a kan zanga-zangar adawa da mulkin soja a ranar 30 ga watan Disamba, kamar yadda ‘yan sandan Sudan suka sanar a ranar Juma’a.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, jami’an tsaro sun harba barkonon tsohuwa da gurneti a yayin da masu zanga-zangar suka bi ta birnin Khartoum da garuruwan Omdurman da Bahri dake makwabtaka da fadar shugaban kasa a jiya Alhamis.

A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar sun ce an kashe mutane hudu a Omdurman, sannan masu zanga-zangar 297 da jami’an ‘yan sanda 49 sun jikkata a fadin kasar a zanga-zangar da ta hada dubun dubatar mutane.

Tashar talabijin ta Al Hadath ta rawaito cewa, mai ba da shawara ga shugaban soji, Abdel Fattah Al-Burhan na cewa, sojoji ba za su bari kowa ya jawo kasar cikin rudani ba, kuma ci gaba da zanga-zangar ta kasance kumfar baki ne, domin haka “ba za su bari kowa ya jefa kasar cikin rudani ba. domin cimma mafita ta siyasa.

Zanga-zangar ta ranar Alhamis ta kasance zagaye na rana 11 na manyan zanga-zangar, tun bayan juyin mulkin ranar 25 ga watan Oktoba da ya sa a ka tsige, Abdallah Hamdok, sannan kuma a ka mayar da shi kan karagar mulki. Sai dai masu zanga-zangar dai sun bukaci sojoji da kada su taka rawar gani a cikin gwamnati a lokacin mika mulki a yayin zabe.

Gamayyar Kungiyoyin ‘Yanci da Sauyi ta ce, jami’an tsaro “Sun yi amfani da danniya fiye da kima” a ranar Alhamis tare da yin kira ga al’ummomin yankuna da na kasa da kasa da kungiyoyin kare hakkin bil’adama da su yi Allah wadai da juyin mulkin.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa Ę“ar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar ʓansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar Ɗangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ʙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ā€˜yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ā€˜yan sandan jihar Kano ta kama wasu ā€˜yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp