fidelitybank

Rana ta 11: Sojoji sun harbe masu zanga-zanga a Sudan

Date:

Jami’an tsaron kasar Sudan sun harbe mutane hudu a wani samame da a ka yi a fadin kasar a kan zanga-zangar adawa da mulkin soja a ranar 30 ga watan Disamba, kamar yadda ‘yan sandan Sudan suka sanar a ranar Juma’a.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, jami’an tsaro sun harba barkonon tsohuwa da gurneti a yayin da masu zanga-zangar suka bi ta birnin Khartoum da garuruwan Omdurman da Bahri dake makwabtaka da fadar shugaban kasa a jiya Alhamis.

A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar sun ce an kashe mutane hudu a Omdurman, sannan masu zanga-zangar 297 da jami’an ‘yan sanda 49 sun jikkata a fadin kasar a zanga-zangar da ta hada dubun dubatar mutane.

Tashar talabijin ta Al Hadath ta rawaito cewa, mai ba da shawara ga shugaban soji, Abdel Fattah Al-Burhan na cewa, sojoji ba za su bari kowa ya jawo kasar cikin rudani ba, kuma ci gaba da zanga-zangar ta kasance kumfar baki ne, domin haka “ba za su bari kowa ya jefa kasar cikin rudani ba. domin cimma mafita ta siyasa.

Zanga-zangar ta ranar Alhamis ta kasance zagaye na rana 11 na manyan zanga-zangar, tun bayan juyin mulkin ranar 25 ga watan Oktoba da ya sa a ka tsige, Abdallah Hamdok, sannan kuma a ka mayar da shi kan karagar mulki. Sai dai masu zanga-zangar dai sun bukaci sojoji da kada su taka rawar gani a cikin gwamnati a lokacin mika mulki a yayin zabe.

Gamayyar Kungiyoyin ‘Yanci da Sauyi ta ce, jami’an tsaro “Sun yi amfani da danniya fiye da kima” a ranar Alhamis tare da yin kira ga al’ummomin yankuna da na kasa da kasa da kungiyoyin kare hakkin bil’adama da su yi Allah wadai da juyin mulkin.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta fitar da sabbin ʙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...

Isra’ila ta amince da sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Isra'ila ta amince...

Buhari ba zai taɓa cin amanar Tinubu ba – Garba Shehu

Tsohon babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai...

Mutane 207 ne suka mutu a ambaliyar Neja – NSEMA

Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta...

Jiga-jigan jam’iyyar PDP za su sauya sheʙa don tunkarar APC a 2027

Wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP da suka hada da tsohon...

Za a ʙaddamar da jam’iyyar hammaya da za ta tunkari APC

Gamayyar jam'iyyun adawa a ranar Talata, ta amince da...

Sojoji sun kashe mayaʙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aʙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...
X whatsapp