Gwamna jihar Zamfara, Bello Matawalle Maradum ya nada karin wasu mukamai 250 na siyasa, domin taimaka wa harkokin mulki a jihar.
Babban daraktan harkokin siyasa da huldar jamâiyyar, Alhaji Mikailu Aliyu ne ya bayyana hakan yayin da ya ke zantawa da manema labarai a Gusau, ranar Laraba.
Aliyu ya ce “Dalilin da ya sa aka nada shi ne, domin tabbatar da cewa shugabanci nagari ya isa ga alâumma da kuma alâumma. Tun da aka kafa gwamnati, gwamnan ya nada kwamishinoni 25, masu ba da shawara na musamman 55, da manyan daraktoci 72 da kuma mambobin hukumar 12”.
Ya kuma ce,”Wadanda aka nada a siyasance 250 sun hada da manyan daraktoci takwas da kuma manyan mataimaka na musamman 242, wanda ya kawo adadin wadanda aka nada a siyasance a jihar zuwa 1,700.