fidelitybank

Gwamnatin Kebbi ta yi hadin gwiwa da Likitocin kasa da kasa

Date:

Kungiyar likitoci mai zaman kanta ba tare da iyaka ba ta kasa da kasa ta kasar Faransa, (Doctors without Borders) ta ce a shirye ta ke ta hada gwiwa da gwamnatin jihar Kebbi, domin isar da ayyukan kiwon lafiya ga al’ummar jihar.

Gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu ne ya karbi bakwancin tawagar karkashin jagorancin shugaban tawagar, Dr Shaukat Muttaqi a gidan gwamnati dake Birnin Kebbi.

A lokacin da ya ke karbar tawagar,  a madadin gwamnan, shugaban ma’aikatan jihar, Alhaji Sulaiman Muhammad Argungu, ya yi maraba da likitocin tare da bayyana farin cikinsa dangane da shirye-shiryen sanya hannu kan yarjejeniyar (MOU) da hadin gwiwa da gwamnati.

Ya kuma tabbatar wa da tawagar cewa, gwamnatin jihar Kebbi za ta samar da yanayi mai kyau, domin gudanar da aikin yadda ya kamata wajen samun kyakkyawan aiki.

Shugaban tawagar, Dr. Shaukat Muttaqi ya bayyana cewa, makasudun ziyarar ta su ita ce, tattauna muhimman ayyukan da suka kiwon lafiya da shirin samar da abinci mai gina jiki da kuma kula da matsalolin al’umm a jihar Kebbi.

A cewarsa, kungiyar Doctors without Borders ta dukufa wajen samar da ayyukan jinya kyauta ga al’ummar jihar Kebbi a shirinta na watanni shida na farko tare da fatan cimma yarjejeniya da ma’aikatar lafiya da jihar Kebbi, domin fara ayyuka cikin gaggawa.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa Æ´ar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar ÆŠangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp