Kungiyar likitoci mai zaman kanta ba tare da iyaka ba ta kasa da kasa ta kasar Faransa, (Doctors without Borders) ta ce a shirye ta ke ta hada gwiwa da gwamnatin jihar Kebbi, domin isar da ayyukan kiwon lafiya ga al’ummar jihar.
Gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu ne ya karbi bakwancin tawagar karkashin jagorancin shugaban tawagar, Dr Shaukat Muttaqi a gidan gwamnati dake Birnin Kebbi.
A lokacin da ya ke karbar tawagar, a madadin gwamnan, shugaban ma’aikatan jihar, Alhaji Sulaiman Muhammad Argungu, ya yi maraba da likitocin tare da bayyana farin cikinsa dangane da shirye-shiryen sanya hannu kan yarjejeniyar (MOU) da hadin gwiwa da gwamnati.
Ya kuma tabbatar wa da tawagar cewa, gwamnatin jihar Kebbi za ta samar da yanayi mai kyau, domin gudanar da aikin yadda ya kamata wajen samun kyakkyawan aiki.
Shugaban tawagar, Dr. Shaukat Muttaqi ya bayyana cewa, makasudun ziyarar ta su ita ce, tattauna muhimman ayyukan da suka kiwon lafiya da shirin samar da abinci mai gina jiki da kuma kula da matsalolin al’umm a jihar Kebbi.
A cewarsa, kungiyar Doctors without Borders ta dukufa wajen samar da ayyukan jinya kyauta ga al’ummar jihar Kebbi a shirinta na watanni shida na farko tare da fatan cimma yarjejeniya da ma’aikatar lafiya da jihar Kebbi, domin fara ayyuka cikin gaggawa.