A daren ranar Talata ne wata hatsaniya ta kaure tsakanin jami’an hukumar Hisbah ta Kano da wasu matasa a wata mashayar Barasa da ke unguwar Sabon Gari a cikin garin Kano.
Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar Hisbah, sun dira a wani wajen shaye-shaye mai suna, Ballat Hughes da ke Court Road a cikin unguwar Sabon Gari.
Hukumar Hisba ta sami rahoton yadda a ke ta’ammali da Giya a wajen, domin kwace Barasa da sauran kayan shaye-shaye.
Lamarin da ya fusata matasan da ke wajen har ta kai ga sun fara jifan ‘yan Hisbah tare da fasa kwalaben giya, wanda ya kai ga samun hatsaniya a wajen.
Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa bayan faruwar lamarin, ‘yan daba da wasu bata gari sun yi amfani da wannan damar inda suka sace wasu muhimman kayayyaki a wajen.
Wannan lamarin ne ya sanya, shugaban hukumar Hisba, Muhammad Harun Ibn Sina, ya magantu, ya ce”Mun samu rahoton faruwar cewa a na tara mata da matasa a na koya musu shan Giya da kwaya a wajen, hakan ne ya sa mu ka kai sumame wajen, amma mun sami nasarar taho da mai siyar da Giyar a wajen, bayan an jefe mu da duwatsu, har da raunata jam’ian mu, kuma za mu gurfanar da mai siyar da Giyar a gaban kotu, domin ta girbi abin da ta shuka”. Inji Ibn Sina.