fidelitybank

Giya: Hisba ta gamu da tutsu yayin sumame

Date:

A daren ranar Talata ne wata hatsaniya ta kaure tsakanin jami’an hukumar Hisbah ta Kano da wasu matasa a wata mashayar Barasa da ke unguwar Sabon Gari a cikin garin Kano.

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar Hisbah, sun dira a wani wajen shaye-shaye mai suna, Ballat Hughes da ke Court Road a cikin unguwar Sabon Gari.

Hukumar Hisba ta sami rahoton yadda a ke ta’ammali da Giya a wajen, domin kwace Barasa da sauran kayan shaye-shaye.

Lamarin da ya fusata matasan da ke wajen har ta kai ga sun fara jifan ‘yan Hisbah tare da fasa kwalaben giya, wanda ya kai ga samun hatsaniya a wajen.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa bayan faruwar lamarin, ‘yan daba da wasu bata gari sun yi amfani da wannan damar inda suka sace wasu muhimman kayayyaki a wajen.

Wannan lamarin ne ya sanya, shugaban hukumar Hisba, Muhammad Harun Ibn Sina, ya magantu, ya ce”Mun samu rahoton faruwar cewa a na tara mata da matasa a na koya musu shan Giya da kwaya a wajen, hakan ne ya sa mu ka kai sumame wajen, amma mun sami nasarar taho da mai siyar da Giyar a wajen, bayan an jefe mu da duwatsu, har da raunata jam’ian mu, kuma za mu gurfanar da mai siyar da Giyar a gaban kotu, domin ta girbi abin da ta shuka”. Inji Ibn Sina.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa ƴar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar Ɗangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp