fidelitybank

Giya: Hisba ta gamu da tutsu yayin sumame

Date:

A daren ranar Talata ne wata hatsaniya ta kaure tsakanin jami’an hukumar Hisbah ta Kano da wasu matasa a wata mashayar Barasa da ke unguwar Sabon Gari a cikin garin Kano.

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar Hisbah, sun dira a wani wajen shaye-shaye mai suna, Ballat Hughes da ke Court Road a cikin unguwar Sabon Gari.

Hukumar Hisba ta sami rahoton yadda a ke ta’ammali da Giya a wajen, domin kwace Barasa da sauran kayan shaye-shaye.

Lamarin da ya fusata matasan da ke wajen har ta kai ga sun fara jifan ‘yan Hisbah tare da fasa kwalaben giya, wanda ya kai ga samun hatsaniya a wajen.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa bayan faruwar lamarin, ‘yan daba da wasu bata gari sun yi amfani da wannan damar inda suka sace wasu muhimman kayayyaki a wajen.

Wannan lamarin ne ya sanya, shugaban hukumar Hisba, Muhammad Harun Ibn Sina, ya magantu, ya ce”Mun samu rahoton faruwar cewa a na tara mata da matasa a na koya musu shan Giya da kwaya a wajen, hakan ne ya sa mu ka kai sumame wajen, amma mun sami nasarar taho da mai siyar da Giyar a wajen, bayan an jefe mu da duwatsu, har da raunata jam’ian mu, kuma za mu gurfanar da mai siyar da Giyar a gaban kotu, domin ta girbi abin da ta shuka”. Inji Ibn Sina.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp