fidelitybank

Daliban Kano 3 sun shiga jerin sahun wadanda a ka fi kafa hujja da su a fanin kimiyya na duniya

Date:

Wasu dalibai 3 da toshon gwamnatin, Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso ta dauki nauyin karatun su, Drs Aliyu Isa Aliyu da Tukur Abdulkadir Sulaiman, da kuma Abdullahi Yusuf, sun shiga cikin jerin sahun gaba na cikin kashi 2 na masana kimiyya wadan da a ka fi nema a duniya.

Jerin sunayen su, wanda a ka buga a watan Agusta 2021, a cikin ƙungiyar masu bincike ne suka shirya wanda, Farfesa John Loannidis na Jami’ar Stanford, California da ke Amurka.

Jerin ya haɗa da masu bincike sama da 100,000 waɗanda a ka zaɓa tsakanin masana kimiyya sama da miliyan 8 a cikin fagagen kimiyya 22 da ƙananan 176 a duk faɗin duniya.

Daily Nigerian ta rawaito cewa, an haifi Dr. Abdullahi Yusuf a karamar hukumar Dala a jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano a shekarar 2010. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) a Applied Mathematics daga jami’ar Firat University, Elazig ta kasar Turkiyya a 2019.

An haifi Dr. Tukur Abdulkadir Sulaiman a karamar hukumar Kiru da ke jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D). wanda ya yi karatu a fannin lisafi na Applied Mathematics a jami’ar Firat, Elazig, Turkiyy a 2019.

An haifi Dr. Aliyu Isa Aliyu a karamar hukumar Bichi ta jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) na Applied Mathematics a jami’ar Firat Elazig, Turkiyya a 2018.

Matasan malaman uku na daga cikin wadanda su ka ci gajiyar tallafin karatu na kasashen waje na gwamnatin jihar Kano a zamanin Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso daga 2011 zuwa 2014. An dauki nauyin karatunsu a shekarar 2012 domin yin digiri na biyu a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jordan da ke Irbid ta kasar Jordan.

Mutanen uku a halin yanzu su na aiki da Sashen Lissafi na Jami’ar Tarayya Dutse da ke Jigawa a Najeriya.

 

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp