Wasu dalibai 3 da toshon gwamnatin, Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso ta dauki nauyin karatun su, Drs Aliyu Isa Aliyu da Tukur Abdulkadir Sulaiman, da kuma Abdullahi Yusuf, sun shiga cikin jerin sahun gaba na cikin kashi 2 na masana kimiyya wadan da a ka fi nema a duniya.
Jerin sunayen su, wanda a ka buga a watan Agusta 2021, a cikin ƙungiyar masu bincike ne suka shirya wanda, Farfesa John Loannidis na Jami’ar Stanford, California da ke Amurka.
Jerin ya haɗa da masu bincike sama da 100,000 waɗanda a ka zaɓa tsakanin masana kimiyya sama da miliyan 8 a cikin fagagen kimiyya 22 da ƙananan 176 a duk faɗin duniya.
Daily Nigerian ta rawaito cewa, an haifi Dr. Abdullahi Yusuf a karamar hukumar Dala a jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano a shekarar 2010. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) a Applied Mathematics daga jami’ar Firat University, Elazig ta kasar Turkiyya a 2019.
An haifi Dr. Tukur Abdulkadir Sulaiman a karamar hukumar Kiru da ke jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D). wanda ya yi karatu a fannin lisafi na Applied Mathematics a jami’ar Firat, Elazig, Turkiyy a 2019.
An haifi Dr. Aliyu Isa Aliyu a karamar hukumar Bichi ta jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) na Applied Mathematics a jami’ar Firat Elazig, Turkiyya a 2018.
Matasan malaman uku na daga cikin wadanda su ka ci gajiyar tallafin karatu na kasashen waje na gwamnatin jihar Kano a zamanin Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso daga 2011 zuwa 2014. An dauki nauyin karatunsu a shekarar 2012 domin yin digiri na biyu a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jordan da ke Irbid ta kasar Jordan.
Mutanen uku a halin yanzu su na aiki da Sashen Lissafi na Jami’ar Tarayya Dutse da ke Jigawa a Najeriya.