Shugaban kasar Amurka, Joe Biden, ya bukaci Amurkawa da su yi watsi da irin karairayin da ya yi musu a jawabin da ya yi a ranar Alhamis don tunawa da cika shekara guda da tayar da rikici na kutsawa fadar gwamnatin Amurka da magoya bayan tsohon shugaban kasar, Donald Trump, su ka yi a ranar 6 ga watan Janairu.
Biden, dan jam’iyyar Democrat, ya kayar da Trump na Republican a zaben 2020, amma tsohon shugaban kasar ya yi karyar cewa an tafka magudi a zaben, kuma jawabin da ya yi makonni biyu gabanin rantsar da Biden da ya bukaci magoya bayansa da su yi fada tare da rura wutar tarzomar da aka yi a Capitol.
Biden da mataimakin shugaban kasa Kamala Harris za su yi magana a Capitol ranar alhamis dinnan kuma Fadar White House ta ce Biden zai dora alhakin ga Trump game da tashin hankalin shekara guda da ta gabata.
Mutane hudu ne suka mutu a ranar tarzomar, yayin da dan sandan Capitol daya ya mutu washegari.