fidelitybank

Mutane 19 sun mutu yayin da 26 suka jikkata a Kano – FRSC

Date:

A kalla mutane 19 ne suka mutu yayin da wasu 26 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a Bagauda kusa da harabar makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya da ke kan hanyar Kano zuwa Zaria.

Kwamandan hukumar kare aukuwar hadura ta kasa FRSC a jihar Kano, Zubairu Mato, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ranar Alhamis a Kano.

Ya ce, hadarin ya rutsa da motocin Hiace guda biyu na kasuwanci mai lamba KBT 152 XA da NSR 275 ZX.

“Mun samu kira da misalin karfe 7:30 na safiyar ranar 6 ga Janairu, 2022. Da samun labarin, mun yi gaggawar aika jami’an mu da motar mu zuwa wurin da lamarin ya faru, domin ceto wadanda abin ya shafa da karfe 7:40 na safe,” in ji Mato.

Kwamandan sashin ya ce, hatsarin ya auku ne, sakamakon gudun wuce kima, lamarin da ya kai ga karo da juna inda motocin biyu suka yi taho mu gama da wuta. Hatsarin ya shafi jimillar fasinjoji 45 a cikin motocin bas guda biyu, daga cikinsu maza 14 da mata hudu sai wani yaro namiji daya da suka rasa rayukansu yayin da wasu 26 suka samu munanan raunuka,” inji shi.

Mato ya ce,”An kai wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kura, domin yi musu magani, yayin da a ka mika gawarwakin sauran ga ‘yan uwansu da ke ofishin ‘yan sanda na Bebeji”. A cewar Mato.

Kwamandan sashen ya shawarci masu ababen hawa da su guji yin gudu, kima a kan ababen hawan su.

 

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp