fidelitybank

Zauren hadin kan Malamai da kungiyoyin addini sun roki KAROTA da ‘yan Adaidaita

Date:

Zauren Hadin Kan Malamai da Kungiyoyin Addinin Musulunci a Jihar Kano sun yi kira ga gwamnatin Jihar da kungiyar direbobin babur mai kafa uku da a ka fi sani da A daidaita Sahu da su sasanta tsakaninsu.

Kiran na zuwa ne a daidai lokacin da yajin aiki direbobin babur din suka fara a Jihar ranar Litinin ya shiga yini na uku.

Cikin zantawa da manema labarai, sakataren Zauren, Dr, Sa’id Ahmad Dukawa ne ya tabbatar da hakan..

Ya ce”Zauren ya damu matuka da halin yajin aikin, matuka baburan ya jefa al’ummar Jihar cikin kangi.

A cewarsa, “Kasancewar wannan yajin aikin ya shafi zirga-zirgar ’yan makaranta da ma’aikata da ’yan kasuwa da marasa lafiya masu zuwa asibiti da sauran al’ummar gari masu bukatu daban-daban, Zauren ya damu matuka da irin hali da al’umma suka shiga a sanadiyyar yajin aikin, musamman duba da yanayin da dama ake ciki na kunci da matsin halin rayuwa.A dalilin hakan, Zaure yana kira ga gwamnati da matuka baburan da su yi la’akari da yanayin da dubban mutane suka fada, su gaggauta zama tare don bibiyar matsalolinsu tare da warware su cikin ruwan sanyi.”

Zauren ya kuma jaddada rokonsa ga bangarorin biyu da su dubi Allah tare da duba halin da al’umma ke ciki na rashin abin hawa a Kano.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp