Zauren Hadin Kan Malamai da Kungiyoyin Addinin Musulunci a Jihar Kano sun yi kira ga gwamnatin Jihar da kungiyar direbobin babur mai kafa uku da a ka fi sani da A daidaita Sahu da su sasanta tsakaninsu.
Kiran na zuwa ne a daidai lokacin da yajin aiki direbobin babur din suka fara a Jihar ranar Litinin ya shiga yini na uku.
Cikin zantawa da manema labarai, sakataren Zauren, Dr, Sa’id Ahmad Dukawa ne ya tabbatar da hakan..
Ya ce”Zauren ya damu matuka da halin yajin aikin, matuka baburan ya jefa al’ummar Jihar cikin kangi.
A cewarsa, “Kasancewar wannan yajin aikin ya shafi zirga-zirgar ’yan makaranta da ma’aikata da ’yan kasuwa da marasa lafiya masu zuwa asibiti da sauran al’ummar gari masu bukatu daban-daban, Zauren ya damu matuka da irin hali da al’umma suka shiga a sanadiyyar yajin aikin, musamman duba da yanayin da dama ake ciki na kunci da matsin halin rayuwa.A dalilin hakan, Zaure yana kira ga gwamnati da matuka baburan da su yi la’akari da yanayin da dubban mutane suka fada, su gaggauta zama tare don bibiyar matsalolinsu tare da warware su cikin ruwan sanyi.”
Zauren ya kuma jaddada rokonsa ga bangarorin biyu da su dubi Allah tare da duba halin da al’umma ke ciki na rashin abin hawa a Kano.