Wata babbar kotun jihar Abia ta sanya ranar 19 ga watan Janairu, domin yanke hukunci kan karar da Nnamdi Kanu, shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, ya shigar a gabanta.
Lauyan Kanu na musamman, Aloy Ejimakor, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Talata.
Idan ba a manta ba an saurari karar kuma an kammala shari’ar ne a ranar 10 ga Disamba, 2021, a gaban mai shari’a, Benson Anya na babbar kotun jihar, Abia da ke Umuahia.
Sanarwar ta Ejimakor ta ce: “Domin samun bayanan manema labarai da sauran jama’a, an sanya ranar 19 ga Janairu, 2022 domin yanke hukunci kan karar Mazi Nnamdi Kanu a gaban babbar kotun jihar Abia.”
Kara da Ejimakor ya kaddamar a madadin Kanu ya roki kotun da ta ayyana farmakin da sojoji su ka kai wa shugaban kungiyar ta IPOB a watan Satumban 2017 a matsayin haramtacce.