fidelitybank

Tsaro: Yawanci daliban bogi ne ke zaune a Danbare – Dr. Idris Rogo

Date:

Shugaban kwamitin tsaro na yankin unguwar Danbare D, a karamar hukumar Kumbotso, Dr. Idris Salisu Rogo, ya ce kusan yankin sun a Danbare yafi kowane waje kalubale a jihar Kano, saboda haka a yanzu haka sun shirya tantance duk wani mutum da zai karbi haya a yankin su.

Dr. Idris Rogo, ya kuma ce a yanzu haka sun hada kai da jami’ar Bayero, domin tantance duk wani dalibi da zai zauna a yankin su.

Dr. Rogo na wannan jawabin ne a lokacin da kungiyar su ta bude sabon ofishin Bijilante, a yankin Danbare.

Ya ce, “Ba za mu yarda Karuwai su tare mana a cikin unguwa ba, saboda haka mun shirya tantance duk wani dalibi a yankin, sakamakon kaso wajen 87 dalibai na bogi ne ke zaune a yankin mu, kuma ba za mu taba yarda da hakan ba, saboda haka mu ka hada hannu da hukumar jami’ar Bayero ta Kano, domin dakile abun”. Inji Dr. Rogo.

A nasa jawabin mai unuguwar yankin, Saifullahi Abba Labaran ya ce,”Mun bude wannan ofishin ne saboda mu dakile duk wasu abubuwan alfasha da a ke gudanarwa a yankin mu, kuma za mu yi aiki tare da ‘yan bijilante, domin samun zaman lafiya mai daurewa a Danbare”.

Da Platinium Post ke tattaunawa da sabon kwamandan yankin Bijilante, Mujitafa Rabilu Muhammad Danbare Dan Inji, ya ce,”Zan yi aiki tsakani na da Allah, saboda na fara aiki ne tun daga matakin kurtu na Bijilante, wanda a yanzu ofishin mu ya zama Unit a tsakiyar gari, za mu yi aiki domin samar da tsaro a Danbare, kuma ba sani ba saboda duk wanda ya yi laifi ko kanina ko dan uwa na za mu ladaftar da su”. Inji Mujitafa.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp