Shugaban kwamitin tsaro na yankin unguwar Danbare D, a karamar hukumar Kumbotso, Dr. Idris Salisu Rogo, ya ce kusan yankin sun a Danbare yafi kowane waje kalubale a jihar Kano, saboda haka a yanzu haka sun shirya tantance duk wani mutum da zai karbi haya a yankin su.
Dr. Idris Rogo, ya kuma ce a yanzu haka sun hada kai da jami’ar Bayero, domin tantance duk wani dalibi da zai zauna a yankin su.
Dr. Rogo na wannan jawabin ne a lokacin da kungiyar su ta bude sabon ofishin Bijilante, a yankin Danbare.
Ya ce, “Ba za mu yarda Karuwai su tare mana a cikin unguwa ba, saboda haka mun shirya tantance duk wani dalibi a yankin, sakamakon kaso wajen 87 dalibai na bogi ne ke zaune a yankin mu, kuma ba za mu taba yarda da hakan ba, saboda haka mu ka hada hannu da hukumar jami’ar Bayero ta Kano, domin dakile abun”. Inji Dr. Rogo.
A nasa jawabin mai unuguwar yankin, Saifullahi Abba Labaran ya ce,”Mun bude wannan ofishin ne saboda mu dakile duk wasu abubuwan alfasha da a ke gudanarwa a yankin mu, kuma za mu yi aiki tare da ‘yan bijilante, domin samun zaman lafiya mai daurewa a Danbare”.
Da Platinium Post ke tattaunawa da sabon kwamandan yankin Bijilante, Mujitafa Rabilu Muhammad Danbare Dan Inji, ya ce,”Zan yi aiki tsakani na da Allah, saboda na fara aiki ne tun daga matakin kurtu na Bijilante, wanda a yanzu ofishin mu ya zama Unit a tsakiyar gari, za mu yi aiki domin samar da tsaro a Danbare, kuma ba sani ba saboda duk wanda ya yi laifi ko kanina ko dan uwa na za mu ladaftar da su”. Inji Mujitafa.