fidelitybank

Tsaro: Yawanci daliban bogi ne ke zaune a Danbare – Dr. Idris Rogo

Date:

Shugaban kwamitin tsaro na yankin unguwar Danbare D, a karamar hukumar Kumbotso, Dr. Idris Salisu Rogo, ya ce kusan yankin sun a Danbare yafi kowane waje kalubale a jihar Kano, saboda haka a yanzu haka sun shirya tantance duk wani mutum da zai karbi haya a yankin su.

Dr. Idris Rogo, ya kuma ce a yanzu haka sun hada kai da jami’ar Bayero, domin tantance duk wani dalibi da zai zauna a yankin su.

Dr. Rogo na wannan jawabin ne a lokacin da kungiyar su ta bude sabon ofishin Bijilante, a yankin Danbare.

Ya ce, “Ba za mu yarda Karuwai su tare mana a cikin unguwa ba, saboda haka mun shirya tantance duk wani dalibi a yankin, sakamakon kaso wajen 87 dalibai na bogi ne ke zaune a yankin mu, kuma ba za mu taba yarda da hakan ba, saboda haka mu ka hada hannu da hukumar jami’ar Bayero ta Kano, domin dakile abun”. Inji Dr. Rogo.

A nasa jawabin mai unuguwar yankin, Saifullahi Abba Labaran ya ce,”Mun bude wannan ofishin ne saboda mu dakile duk wasu abubuwan alfasha da a ke gudanarwa a yankin mu, kuma za mu yi aiki tare da ‘yan bijilante, domin samun zaman lafiya mai daurewa a Danbare”.

Da Platinium Post ke tattaunawa da sabon kwamandan yankin Bijilante, Mujitafa Rabilu Muhammad Danbare Dan Inji, ya ce,”Zan yi aiki tsakani na da Allah, saboda na fara aiki ne tun daga matakin kurtu na Bijilante, wanda a yanzu ofishin mu ya zama Unit a tsakiyar gari, za mu yi aiki domin samar da tsaro a Danbare, kuma ba sani ba saboda duk wanda ya yi laifi ko kanina ko dan uwa na za mu ladaftar da su”. Inji Mujitafa.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp