Shugaban kungiyar masana’antar Kanywood, Alhassan Kwalle, ya barranta masana’antar su a kan wani shirin fim da a yanzu haka a ke tallansa a shafin YouTube.
Alhassan Kwalle ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai a kan sabon fim din da a ka far ace-ce-kuce a kan sa.
Alhassan Kwalle ya ce,”Shirin ya sabawa koyarwa ta addinin Musulci da al’adun Hausawa da kuma dokokin masana’antar, domin haka mun barranta kan mu da fim din. Kuma za mu tabbatar da cewa za mu dauki matakan da ya dace na shari’a a kan wanda ya shirya fim din ,duk da mashiryin shirin ba dAn masana’antar mu ba ne.
“Mun yi waya da mashiryin shirin, domin in sanar da shi cewa abun ba dai-dai bane, Amma tun farko ya ce shi fa ba dan Kanywood ba ne, ya shirya shirin ne a karan kansa. Ina da yakinin hukumar tace fina-finan ta jihar Kano ba za ta bar abun sakakaba, yasan za ta dauki matakin da ya dace, domin hana fitar da fim din gudun lalata tarbiyyar al’umma”. Inji Alhassan.
A Jawabinsa shugaban hukumar tace fina-finan Hausa da Dab’I ta Jihar Kano, Isma’ila Na-Abba afakallah, ya ce, ba za mu lamunci irin badalar cikin fina-finan ba, ina da tabbacin hukumar mu za ta nemi mashiryin shirin fim din, domin gurfanar da shi a gaban shari’a. Aikin hukumar ne ta ha na yin fim din da ya sabawa addinin Musulci da al’adun Malam Bahaushe, domin tabbatar da sauke nauyin da Gwamnati ta dora wa hukumar.
Shirin fim din mai suna Makaranta ya dai yamutsa hazo tun bayan sakin tallan kadan daga cikin wani bangaren sa a shafin Youtube.