Rundunar ƴan sandan Jihar Zamfara ta kama wata mata da ake zargi da yunƙurin sayar da yaro ɗan shekara biyu.
Jaridar Punch ta rawaito cewa, kwamishinan ƴan sanda na jihar, Ayuba Elkana ya ce, an kama matar ne tun a ranar 8 ga watan Janairu a yankin Tullukawa da ke Gusau inda ake zargin matar da yunƙurin sayar da ɗan kishiyarta.
Matar wadda asalinta mutumiyar ƙauyen Danyade ce, da ke Maradi a Jamhuriyyar Nijar, an kama ta ne ɗauke da ɗan kishiyarta wadda ta shaida wa jami’an tsaro cewa, ta sato yaron ne daga wajen kishiyarta, domin ita ma ta rama sata da sayar da ɗanta da kishiyarta ta yi a baya.
Amma daga baya ta ƙara shaida wa jami’an tsaro cewa, ta yi yunƙurin sayar da yaron ne, domin samun kuɗin biyan buƙatunta na yau da kullum.
Rundunar ƴan sandan ta ce, za a miƙa wadda ake zargi zuwa ga hukumar kula da shige da fice ta Najeriya domin zurfafa bincike.