fidelitybank

Jigawa ta hana yin fim da wakokin soyayya da na siyasa a jihar

Date:

Hukumar tace fina-finai ta jJihar Jigawa ta ce masu shiryawa da daukar fim, ko rera wakoki na siyasa da na soyyaya ko na fim, da masu yi musu rawa da su dakatar da harkokinsu a jihar har sai sun yi rijista da hukumar.

Daraktan hukumar tace fina-finai ta jihar, Yusuf Magaji, ya shaida wa BBC cewa sun dauki matakin ne bayan daraktan fim din nan mai suna ‘Makaranta’ ya bayyana cewa a jihar ya dauki fim din.

Fim din ‘Makaranta’ ya nuna abubuwa da dama da É—umbin jama’a suke ganin ba su dace a yi fim a kansu ba, wadanda suka hada da madigo da batsa da makamatansu.

“Mun yi haka ne saboda mu tantance wadanda suke shigowa jihar. Akwai wani fim da aka shirya wai shi ‘Makaranta’ inda shi wanda ya shirya shi jihar Kano take nemansa ruwa a jallo. sai yake cewa ba a Kano ya shirya ba, a Jigawa ne. A gaskiya bai zo wurinmu ya nemi izinin shirya fim din ba,” a cewar Yusuf Magaji.

Ya kara da cewa daraktan ya yi furucin ne da zummar shafa wa Jigawa kashin-kaji, domin haka su ma daga yanzu ba za su bari a rinka yin abubuwan da suka keta dokoki da al’adun jiharsu ba.

Masu shirya fina-finai masu dogon zango sun bayyana amincewarsu da wadannan matakai da gwamnatocin jihohin Kano da Jigawa suka dauka, suna masu yaba wa matakan.

Lawan Ahmad, tauraron fim ne kuma mai shirya fim din dogon zango na Izzar So, kuma ya shaida mana cewa su dama sai sun mika fina-finansu an tantance kafin su sanya a YouTube.

“Mu dama can muna bayar da fina-finan mu a duba. Sai dai idan an samu tsaiko ko wata matsala saboda yanayin aiki shi ne za ka ga ba mu bayar ba. Amma maganar gaskiya yadda wasu suke amfani da YouTube wajen saka abubuwan da ba su dace ba, ya kamata a sanya musu ido,” in ji shi.

A cewarsa matakin da hukumar tace fina-finai ta dauka yana da amfani “saboda kare al’ada da addininmu.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp