fidelitybank

‘Yan sanda sun gayyaci tsohon kwamishinan gwamnatin Ganduje

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta gayyaci tsohon kwamishinan ayyuka a gwamnatin gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Muazu Magaji.

Da ya ke zantawa da Aminiya, Magaji ya ce, ofishin siyasa na hukumar SBI ne ya gayyace shi, amma ba su bayyana masa mene ne makasudin gayyatar ba.

“Na sami waya cewa suna son in bayyana a gabansu. Na tambaye su a kan menene ? kuma suka ce min zan san duk abubuwan da ke faruwa idan na zo.

“Lokacin da na je sai suka ce, gwamnatin jihar Kano ce ta kai kara ta,” inji shi.Da aka tambaye shi ko ya mutunta gayyatar? Tsohon kwamishinan ya ce, “A yanzu haka ina Abuja, kuma zan mutunta gayyatar da zarar na isa Kano a ranar Talata.

“Me nake gudu? Tabbas zan girmama gayyatar gobe,” ya tabbatar.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa bai samu, cewa uffan ba game da lamarin.

Magaji dai ya sha cece-kuce tun bayan da aka kore shi daga mukamin kwamishinan ayyuka.

Gwamnan ya sa ke nada shi a matsayin mai taimaka masa kan bututun iskar gas na AKK, amma ya kore shi daga baya.

Tun daga wancan lokacin tsohon kwamishinan da aka kora ya rinka sukar Ganduje da gwamnatinsa a Facebook.

A halin yanzu, Magaji dan tsagin Shekarau ne na jam’iyyar APC.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp