fidelitybank

‘Yan sanda sun gayyaci tsohon kwamishinan gwamnatin Ganduje

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta gayyaci tsohon kwamishinan ayyuka a gwamnatin gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Muazu Magaji.

Da ya ke zantawa da Aminiya, Magaji ya ce, ofishin siyasa na hukumar SBI ne ya gayyace shi, amma ba su bayyana masa mene ne makasudin gayyatar ba.

“Na sami waya cewa suna son in bayyana a gabansu. Na tambaye su a kan menene ? kuma suka ce min zan san duk abubuwan da ke faruwa idan na zo.

“Lokacin da na je sai suka ce, gwamnatin jihar Kano ce ta kai kara ta,” inji shi.Da aka tambaye shi ko ya mutunta gayyatar? Tsohon kwamishinan ya ce, “A yanzu haka ina Abuja, kuma zan mutunta gayyatar da zarar na isa Kano a ranar Talata.

“Me nake gudu? Tabbas zan girmama gayyatar gobe,” ya tabbatar.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa bai samu, cewa uffan ba game da lamarin.

Magaji dai ya sha cece-kuce tun bayan da aka kore shi daga mukamin kwamishinan ayyuka.

Gwamnan ya sa ke nada shi a matsayin mai taimaka masa kan bututun iskar gas na AKK, amma ya kore shi daga baya.

Tun daga wancan lokacin tsohon kwamishinan da aka kora ya rinka sukar Ganduje da gwamnatinsa a Facebook.

A halin yanzu, Magaji dan tsagin Shekarau ne na jam’iyyar APC.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp