Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta gayyaci tsohon kwamishinan ayyuka a gwamnatin gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Muazu Magaji.
Da ya ke zantawa da Aminiya, Magaji ya ce, ofishin siyasa na hukumar SBI ne ya gayyace shi, amma ba su bayyana masa mene ne makasudin gayyatar ba.
“Na sami waya cewa suna son in bayyana a gabansu. Na tambaye su a kan menene ? kuma suka ce min zan san duk abubuwan da ke faruwa idan na zo.
“Lokacin da na je sai suka ce, gwamnatin jihar Kano ce ta kai kara ta,” inji shi.Da aka tambaye shi ko ya mutunta gayyatar? Tsohon kwamishinan ya ce, “A yanzu haka ina Abuja, kuma zan mutunta gayyatar da zarar na isa Kano a ranar Talata.
“Me nake gudu? Tabbas zan girmama gayyatar gobe,” ya tabbatar.
Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa bai samu, cewa uffan ba game da lamarin.
Magaji dai ya sha cece-kuce tun bayan da aka kore shi daga mukamin kwamishinan ayyuka.
Gwamnan ya sa ke nada shi a matsayin mai taimaka masa kan bututun iskar gas na AKK, amma ya kore shi daga baya.
Tun daga wancan lokacin tsohon kwamishinan da aka kora ya rinka sukar Ganduje da gwamnatinsa a Facebook.
A halin yanzu, Magaji dan tsagin Shekarau ne na jam’iyyar APC.