fidelitybank

Direban Tireloli sun kashe hanya a Gombe sakamakon harbin abokin aikin su

Date:

Gwamnatin jihar Gombe ta yi kira da a al’ummar jihar da su kwantar da hankula, bayan wani dan sanda da ya harbe wani direban motar Tanka a lokacin da aka samu rashin jituwa a hanyar Gombe ta Dukku zuwa Darazo.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Julius Ishaya Lepes da takwaransa na ma’aikatar tsaron cikin gida da wayar da kan jama’a, Adamu Kupto Dishi ne suka yi wannan kiran yayin ganawa da manema labarai da yammacin Litinin.

Julius ya ce,”Harbin ya faru ne a lokacin da aka samu rashin jituwa lokacin da direban tankar (Abdullahi Bello) ya ki amincewa da umarnin dan sandan ga direban Tankar da ya sauko daga motarsa a shingen binciken ‘yan sanda da ke mahadar Hashidu a safiyar ranar Litinin, bayan harbe-harbe, wasu direbobin Tankar dakon man ne nan take suka tattara tankunansu tare da tare hanyar na tsawon sa’o’i da dama, domin nuna goyon bayansu ga abokin aikinsu wanda ya haifar da hatsaniya a kan babbar hanyar da ta hada Gombe da Bauchi ta hanyar Darazo da sauran jihohin Arewa maso Yamma”. Acewar su.

Ya ce, gwamnati ta sa baki cikin gaggawa, domin dakile doka da oda, saboda an kwancewa dan sandan makamai tare da kama shi, inda ya ce, a halin yanzu hukumomin ‘yan sanda a Gombe na gudanar da bincike, domin gano musabbabin faruwar lamarin.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp