Gwamnatin jihar Gombe ta yi kira da a al’ummar jihar da su kwantar da hankula, bayan wani dan sanda da ya harbe wani direban motar Tanka a lokacin da aka samu rashin jituwa a hanyar Gombe ta Dukku zuwa Darazo.
Kwamishinan yada labarai na jihar, Julius Ishaya Lepes da takwaransa na ma’aikatar tsaron cikin gida da wayar da kan jama’a, Adamu Kupto Dishi ne suka yi wannan kiran yayin ganawa da manema labarai da yammacin Litinin.
Julius ya ce,”Harbin ya faru ne a lokacin da aka samu rashin jituwa lokacin da direban tankar (Abdullahi Bello) ya ki amincewa da umarnin dan sandan ga direban Tankar da ya sauko daga motarsa a shingen binciken ‘yan sanda da ke mahadar Hashidu a safiyar ranar Litinin, bayan harbe-harbe, wasu direbobin Tankar dakon man ne nan take suka tattara tankunansu tare da tare hanyar na tsawon sa’o’i da dama, domin nuna goyon bayansu ga abokin aikinsu wanda ya haifar da hatsaniya a kan babbar hanyar da ta hada Gombe da Bauchi ta hanyar Darazo da sauran jihohin Arewa maso Yamma”. Acewar su.
Ya ce, gwamnati ta sa baki cikin gaggawa, domin dakile doka da oda, saboda an kwancewa dan sandan makamai tare da kama shi, inda ya ce, a halin yanzu hukumomin ‘yan sanda a Gombe na gudanar da bincike, domin gano musabbabin faruwar lamarin.