Wasu ‘yan bindiga wadanda ba a iya gano ko su wanene ba, sun harbe wani mutum a Enugu babban birnin Jihar a safiyar yau Litinin.
Mutanen ɗauke da makamai sun fara harbe-harbe tare da cinna wa wasu gidaje wuta, har su ka kashe wani jami’n tsaro na sa-kai.
Ya zuwa yanzu jami’an tsaro sun isa yankin Greece yayin da a ka tura su yankuna daban-daban na birnin.
BBC ta rawaito cewa, wani bidiyo da a ka yaɗa a shafukan sada zumunta ya nuna yadda mutane ke gudun tsira da rayukansu.
An zargi ƙungiyar ‘yan aware ta IPOB da kai harin yayin da su ke ƙoƙarin tabbatar da dokar hana fita a duk Litiin da su ka saka, sai dai ƙungiyar ta musanta zargin ta na mai cewa ta soke dokar da ta kafa.
Lamarin ya tilasta wa mazauna Enugu rufe shaguna da wuraren harkokinsu domin tsira da rayukansu.