fidelitybank

A saki kadarorin kudaden Afghanistan – Iran

Date:

Kasar Iran ta bukaci gwamnatin Taliban da ta bude kadarorin kudaden Afghanistan da a ka toshe tun bayan da Taliban ta karbe iko da sako su.

A cewar wani kamfanin dillancin labarai na kasar, bayan ganawarsa da mukaddashin ministan harkokin wajen Afghanistan Amir Khan Muttaqi.

Ministan harkokin wajen kasar Iran, Hossein Amirabdollahian ya bayyana cewa, kadarorin kasar Afghanistan da Amurka ta toshe cewa kamata a yi amfani da su wajen gudanar da ayyukan jin kai da kuma kyautata yanayin rayuwa a Afghanistan.

Yakin da jajirtattun al’ummar Afganistan su ka yi ya nuna cewa, babu wani karfi na waje da zai iya mamaye kasar ta Afganistan kuma ya yi mulki a can,” in ji shi.

A ranar 15 ga watan Agusta ne mayakan Taliban masu tsattsauran ra’ayin Islama suka karbe iko da kasar Afganistan a daidai lokacin da sojojin Amurka da na kasashen waje suka janye, bayan shafe shekaru 20 suna goyon bayan gwamnatin Kabul da ke samun goyon bayan kasashen Yamma.

Tuni dai gwamnatocin kasashen waje suka dukufa wajen tsara yadda za su hada kai da kungiyar Taliban, domin kaucewa tabarbarewar tattalin arziki da tsaro a Afghanistan tare da kaucewa amincewa da sabuwar gwamnati a hukumance.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa Æ´ar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar ÆŠangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp