Kasar Iran ta bukaci gwamnatin Taliban da ta bude kadarorin kudaden Afghanistan da a ka toshe tun bayan da Taliban ta karbe iko da sako su.
A cewar wani kamfanin dillancin labarai na kasar, bayan ganawarsa da mukaddashin ministan harkokin wajen Afghanistan Amir Khan Muttaqi.
Ministan harkokin wajen kasar Iran, Hossein Amirabdollahian ya bayyana cewa, kadarorin kasar Afghanistan da Amurka ta toshe cewa kamata a yi amfani da su wajen gudanar da ayyukan jin kai da kuma kyautata yanayin rayuwa a Afghanistan.
Yakin da jajirtattun al’ummar Afganistan su ka yi ya nuna cewa, babu wani karfi na waje da zai iya mamaye kasar ta Afganistan kuma ya yi mulki a can,” in ji shi.
A ranar 15 ga watan Agusta ne mayakan Taliban masu tsattsauran ra’ayin Islama suka karbe iko da kasar Afganistan a daidai lokacin da sojojin Amurka da na kasashen waje suka janye, bayan shafe shekaru 20 suna goyon bayan gwamnatin Kabul da ke samun goyon bayan kasashen Yamma.
Tuni dai gwamnatocin kasashen waje suka dukufa wajen tsara yadda za su hada kai da kungiyar Taliban, domin kaucewa tabarbarewar tattalin arziki da tsaro a Afghanistan tare da kaucewa amincewa da sabuwar gwamnati a hukumance.