fidelitybank

Tsohon kakakin PDP Olisah Metuh ya nemi yafiya da rokon lafiyar sa

Date:

Tsohon mai magana da yawun jam’iyyar PDP, Olisa Metuh, ya bukaci jama’a da su yi masa addu’a kan halin da yake ciki a halin yanzu na rashin lafiya.

Metuh ya roki jama’a da su yafe masa duk wani abu na bacin rai da ya yi a lokacin da yake kan ganiyarsa, musamman ma kalaman sa na fagen siyasa, tare da yi masa addu’ar Allah ya ba shi lafiya.

Olisah Metuh, Ya bayyana cewa, ya samu wasu labarai masu ban tsoro daga likitocinsa, amma ya ce, ya na fatan Allah ya shiga lamarin sa, domin haka ya roki ‘yan Najeriya da su yi masa addu’a.

Metuh na wannan rokon ne a shafukansa na sada zumunta a ranar Juma’a, 21 ga Janairu, 2022, tare da hotonsa a gadon asibiti, bayan an yi masa aikin tiyata.

Ya ce, “A cikin shekara daya an yi min tiyata da yawa, kuma na yi imani da Allah wannan zai zama na karshe. Duk irin fushin da ku ka yi game da furuci na a lokacin da na ke kalamai na na gatse, don Allah ku yi min addu’a”. A cewar Metuh.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp