Tsohon mai magana da yawun jam’iyyar PDP, Olisa Metuh, ya bukaci jama’a da su yi masa addu’a kan halin da yake ciki a halin yanzu na rashin lafiya.
Metuh ya roki jama’a da su yafe masa duk wani abu na bacin rai da ya yi a lokacin da yake kan ganiyarsa, musamman ma kalaman sa na fagen siyasa, tare da yi masa addu’ar Allah ya ba shi lafiya.
Olisah Metuh, Ya bayyana cewa, ya samu wasu labarai masu ban tsoro daga likitocinsa, amma ya ce, ya na fatan Allah ya shiga lamarin sa, domin haka ya roki ‘yan Najeriya da su yi masa addu’a.
Metuh na wannan rokon ne a shafukansa na sada zumunta a ranar Juma’a, 21 ga Janairu, 2022, tare da hotonsa a gadon asibiti, bayan an yi masa aikin tiyata.
Ya ce, “A cikin shekara daya an yi min tiyata da yawa, kuma na yi imani da Allah wannan zai zama na karshe. Duk irin fushin da ku ka yi game da furuci na a lokacin da na ke kalamai na na gatse, don Allah ku yi min addu’a”. A cewar Metuh.