fidelitybank

Tsarin Karba-Karba: A mika shugabanci zuwa Kudu a 2023 – Ngige

Date:

Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Sanata Chris Ngige, ya yi kira da a samar da shugaban kasa daga Kudancin kasar gabanin zaben shugaban kasa na 2023.

Ya kara da cewa, shiyya-shiyya da karba-karba na samar da zaman lafiya, hadin kai, daidaito, ci gaba, amincewa, kishin kasa da kuma tabbatar da cewa babu wata kabila ko wani bangare na kasar da ya mamaye wani.

TheWill ta rawaito cewa, da ya ke amsa tambayoyi daga manema labarai a gidan sa da ke garin Alor na jihar Anambra, Ngige ya dage da cewa, akwai yarjejeniya da ba a rubuta ba tsakanin ‘yan siyasa da jam’iyyun siyasa cewa, ya kamata a yi na karba-karba na ofisoshi, kuma a bangaren jam’iyyar PDP an rubuta a cikin kundin tsarin mulkin ta.

Ministan ya ce, ba a rubuta mika mulki karara a cikin kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC. Sai dai ya nuna cewa kundin tsarin mulki na 1999 kamar yadda a ka yi wa kwaskwarima ya na goyon bayan karban mukamai na siyasa.

Ya kawo misali da sashe na 14 (3) na kundin tsarin mulkin kasar wanda ya bayyana karara kan yadda a ke tafiyar da gwamnati a matakin kasa, jihohi da ma kananan hukumomi, ta yadda bai kamata a samu hakikanin ko ra’ayin mamayar wata kabila ko kungiya daya ba na mutanen da suka fito daga wata kabila guda domin samar da kwarin gwiwa da kishin kasa.

A cewar Ngige, “Mulki da kuma rabon ofisoshi na adalci a kowane mataki na sassan tarayya ya samo asali ne daga wannan tanadi. Domin haka a zahiri, dukkanmu mun yarda, daga wannan kundin tsarin mulkin cewa gwamnati a kowane mataki, majalisa, zartaswa har ma da bangaren shari’a, yakamata ya nuna yaduwar kasa ta yadda babu wata kungiya ta musamman ta mamaye sauran.

 “A jam’iyyun siyasa idan kana da shugaban da ya fito daga Kudu, sakataren ya tafi Arewa. Ka na kuma da Mataimakin Shugaban da ya fito daga Arewa. A wasu wuraren kuma suna da mataimakan shugabanni biyu na Arewa da Kudu. Domin haka, duk waɗannan da aka sanya a cikin cikakken kwandon iko, suna nuna muku cewa an gane cewa saboda bambancin mu, muna buƙatar samun dandalin haɗin kai a cikin bambancin.

“Haka kuma a duk lokacin da shugaban kowace jam’iyyar siyasa ya fito daga Kudu, ana yin duk mai yiwuwa dan takarar shugaban kasa ya fito daga Arewa. Hakazalika, akwai wannan shiri da ake yi na tabbatar da cewa mulki ya koma Arewa a duk lokacin da Shugaban kasa daga Kudu ya yi mulki na tsawon shekaru takwas, akasin haka.

“Na ci gaba da yin tsokaci kan abubuwan da suka faru a baya domin wadanda suka shiga siyasa su san tushen wasu tarurrukan. A lokacin da muka kafa jam’iyyar PDP, an amince cewa shugaban kasa ya tafi Kudu. Amma marigayi Abubakar Rimi ya ce a’a, dole ne ya tsaya takara.

“Na tuna Audu Ogbeh, Cif Sunday Awoniyi, Baba Solomon Lar da sauran su, suka kai Rimi wani lungu a gidan Jerry Gana domin tattaunawa da shi, amma har yanzu Rimi ya dage da tsayawa takara. Sunday Awoniyi wanda dukkan mu muke so da mutuntawa ya fara kuka. Awoniyi, cikin kuka, ya ce dagewar da Rimi ya yi ba shine abin da iyayen da suka kafa Nijeriya suka yi hasashe ba ga kasar. Kun san ya kasance sakataren sirri na firimiya na yankin Arewa a lokacin. Mun kasance sababbi a siyasa a lokacin. Ni da Farfesa ABC Nwosu mun kasance muna ɗaukar jakar Alex Ekwueme zuwa taro. Don haka, mu shaidu ne masu rai kan wannan.”

Ya tuna cewa Rimi ya je Jos ne ya dage sai ya tsaya takara amma saboda shiyya-shiyya aka hana shi takara. Ya janye takararsa ne a wurin taron, inda ya bar ‘yan takarar kudancin kasar kamar Cif Olusegun Obasanjo, Alex Ekwueme, Jim Nwobodo da dai sauran su ne kawai suka yi watsi da shi domin neman tikitin PDP.

“Hakazalika a cikin APP, mun sa Ogbonnaya Onu, Olu Falae da hamshakin attajirin nan na Ibadan, Cif Harry Akande, suka yi watsi da shi. Umaru Shinkafi da sauran masu neman Arewa sun sauka. Domin haka, ba labari ba ne a tarihin siyasar Najeriya ka karkata akalar mulkin wuri guda”. Inji Ngige.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp