fidelitybank

Shirin komawar Kwankwaso APC: Mu na yi masa maraba da zuwa APC – Sanata Babafemi

Date:

Mai baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara kan harkokin siyasa, Sanata Babafemi Ojudu, ya ce, su na yi wa tsohon gwamnan jihar Kano, Dr. Rabi’u Kwankwaso marababa zuwa jam’iyyar APC, har idan rahoton ficewar sa ya tabbata.

Akwai rahotanni da ba a tabbatar da su ba na cewa Kwankwaso ya koma APC a shafukan sada zumunta.

Yayin da ake ta rade-radin sauya shekar Kwankwaso daga jam’iyyar PDP zuwa APC, Ojodu ya bayyana tsohon gwamnan a matsayin “babban mai wayar da kan jama’a, kuma cikakken dan siyasa”.

Ojudu, wanda dan majalisar dattawa ne mai wakiltar mazabar Ekiti ta tsakiya a jihar Ekiti, ya bayyana hakan a shafin Facebook, inda ya makala hoton Kwankwaso, mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da kansa.

Ya kara da cewa, “Labarin ya ba ko’ina cewa, shugaban kungiyar Kwakwansiya, mai girma Sanata Rabiu Kwakwanso ya dawo jam’iyyar mu ta APC. Har yanzu ban tabbatar da hakan ba, amma idan gaskiya ne mu na maraba da zuwan shi.

“Haka zalika wannan zai zama mafi kyawu a harkar siyasar sa. Babban mai wayar da kan jama’a, haziki, kuma hazikin dan siyasa, Kwankwaso ne jagoran jama’a masu jan hula. Zai zama babban kari ga yunkurinmu na samar da Najeriya mai girma.”

Sa’o’i kadan bayan jita-jitar sauya shekar tasa, Kwankwaso a wata hira da ya yi da shi ya yi nuni da yiwuwar komawar sa APC.

Da a ka tambaye shi ko zai iya komawa APC, sai ya amsa da cewa, “A siyasa komai na iya yiwuwa a wannan yanayi. Ba ma son kowane maƙiyi na dindindin. Abin da mu ke so abokai ne na dindindin. Ya na da matukar muhimmanci. Muna aiki domin abota.

“Zai ba ka mamaki cewa wasu abokai na da mu ka fara aiki da su shekaru 30 da su ka wuce, yawancinsu suna nan a raye kuma muna tare. Hatta wadanda suka mutu daga shekaru 30 da su ka gabata zuwa yau suna cikin tarihinmu kuma kowace shekara, muna yin abu ɗaya. Domin haka, a cikin 2023, na yi imanin abubuwa da yawa na iya faruwa.” Inji Ojudu.

 

 

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp