Shugaba Donald Trump na Amurka ya bayar da umarnin dakatar da dukanin ma’aikatan tarayya da ke aiki a ƙarƙashin shirye-shiryen da suka shafi masu neman jinsi ɗaya da dangoginsu (LGBTQ+), da kuma sauran rukunin jama’a da ake mayarwa baya a dangi.
A wata sanarwa da ta fito daga ofishin kula da ma’aikatan ƙasar da aka sanya a shafin X, Shugaban ya bayar da umarnin tura ma’akatan hutu nan take amma kuma za a ci gaba da biyansu albashi.
Matakin ya biyo bayan wannan doka ta shugaban ƙasa da gwamnatin ta Trump ta bayar, wadda ta nemi kawo ƙarshen abin da ta kira kawo ƙarshen tsare-tsare da shirye-shirye masu haɗari da rashin ɗa’a.
Shirye-shiryen da waɗannan ma’aikata ke gudanarwa sun shafi rukunin jama’a da galibi ba su da rinjaye a cikin al’umma kuma sukan fuskanci wariya ko nuna bambanci ko rashin wakilci a wuraren aiki – misali saboda jinsinsu ko ƙabilarsu ko addininsu da makamantansu.