fidelitybank

TAJBANK ya zama gwarzon bankin musulunci na shekara

Date:

Bankin da baya ta’ammali da kuɗin ruwa, TAJBank ya zama shine gwarzon bankin musulunci na shekara.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa TAJBank ya lashe kyautar ne a wani bikin bada kyaututtuka na shekara ga bankuna da sauran ma’aikatun harkar kuɗaɗe na BAFI 2021, da jairdar BusinessDay ta gudanar.

Wannan kyautar ta zo ne watanni biyu bayan da bankin ya lashe kyautar gwarzon shekara da jaridar Leadership ta gudanar.

Mahukunta a kamfanin BusinessDay, a wata sanarwar da su ka fitar, sun ce TAJBank ya lashe kyautar ne sakamakon ƙir-ƙire na harkar banki da ya ke yi da kuma yadda ya ke daɗaɗawa abokan hulɗarsa.

Sanarwar ta ce” TAJBank ya bada mamaki a harkar banki bayan kafa shi a 2019.

“Yadda bankin ya kawo sauyi mai kyau da kuma ƙirƙire-ƙirƙire da wasu tsare-tsare ma zamani da kuma yadda ya ke bunƙasa harkar kuɗaɗe da daɗaɗawa abokan hulɗa, ya bada mamaki ƙwarai,”

Mahukuntan kuma sun yi hasashen cewa nan da 2021 zuwa 2026, harkar bankin musulunci za ta samu bunƙasa da kaso 15 cikin ɗari.

Jaridar ta kara da cewa in dai TAJBank ya sami lasisin yin harkar banki na ƙasa, to zai ƙara bunƙasa da kashi 65 cikin 100.

Da ya ke bayani bayan bada lambar girman, shugaban TAJBank, Hamid Joɗa ya nuna cewa nasarar ta nuna cewa lallai bankin ma kan hanyarsa ta ƙoƙarin bunƙasa harkar banki maras ruwa a Nijeriya.

 

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp