fidelitybank

Siyasa: Atiku zai san matsayin sa na tsayawa takara a sabuwar shekara

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta sanya ranar 21 ga watan Fabrairun 2022, domin yanke hukunci kan ko tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya cancanci tsayawa takarar shugaban Kasa ko a’a.

Mai Shari’a, Inyang Ekwo ne ya sanya ranar da hakan a ranar Litinin, bayan kammala sauraron muhawara tsakanin lauyoyin bangarorin Biyu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa wani kamfani mai zaman kansa mai suna EMA ne ya maka Atikun da jam’iyyar PDP da hukumar zabe (INEC) da kuma Babban Lauyan gwamnatin tarayya a gaban kotun.

Kamfanin dai na kalubalantar cancantar Atikun ta tsayawa takarar shugaban kasa, bisa hujjar cewa ba asalin dan Najeriya ba ne ta nasabar haihuwa.

Ya roki kotun da ta yi la’akari da tande-tanaden sashi na 25 Daya cikin baka (1) da Biyu cikin baka (2) da kuma 131 (a) na kundin tsarin mulki wajen hana shi takarar.

A baya dai gwamnatin jihar Adamawa ta roki kotun da ta saka ta cikin wadanda ake tafka shari’ar da su, inda a ranar 27 ga watan Yulin 2021 kotun ta maince da hakan.

Jihar dai ta shaida wa kotun cewa Atikun ya cancanci tsayawa takara, kuma har ya taba jagorantar Jihar da kuma zama mataimakin shugaban kasa na tsawon shekara Takwas.

To sai dai lauyan masu kara, Oladimeji ya ce ko da ya ke a Najeriya aka haifi Atiku, hakan ba yana nufin shi dan Najeriya ba ne.

A cewarsa, kasancewar an yi kuskure a baya, ba ya nufin a sake maimaita hakan a yanzu.

Daga nan ne Mai Shari’a, Ekwo ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 21 ga watan Fabrarirun 2022 domin yanke hukunci.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp