fidelitybank

Siyasa: Atiku zai san matsayin sa na tsayawa takara a sabuwar shekara

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta sanya ranar 21 ga watan Fabrairun 2022, domin yanke hukunci kan ko tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya cancanci tsayawa takarar shugaban Kasa ko a’a.

Mai Shari’a, Inyang Ekwo ne ya sanya ranar da hakan a ranar Litinin, bayan kammala sauraron muhawara tsakanin lauyoyin bangarorin Biyu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa wani kamfani mai zaman kansa mai suna EMA ne ya maka Atikun da jam’iyyar PDP da hukumar zabe (INEC) da kuma Babban Lauyan gwamnatin tarayya a gaban kotun.

Kamfanin dai na kalubalantar cancantar Atikun ta tsayawa takarar shugaban kasa, bisa hujjar cewa ba asalin dan Najeriya ba ne ta nasabar haihuwa.

Ya roki kotun da ta yi la’akari da tande-tanaden sashi na 25 Daya cikin baka (1) da Biyu cikin baka (2) da kuma 131 (a) na kundin tsarin mulki wajen hana shi takarar.

A baya dai gwamnatin jihar Adamawa ta roki kotun da ta saka ta cikin wadanda ake tafka shari’ar da su, inda a ranar 27 ga watan Yulin 2021 kotun ta maince da hakan.

Jihar dai ta shaida wa kotun cewa Atikun ya cancanci tsayawa takara, kuma har ya taba jagorantar Jihar da kuma zama mataimakin shugaban kasa na tsawon shekara Takwas.

To sai dai lauyan masu kara, Oladimeji ya ce ko da ya ke a Najeriya aka haifi Atiku, hakan ba yana nufin shi dan Najeriya ba ne.

A cewarsa, kasancewar an yi kuskure a baya, ba ya nufin a sake maimaita hakan a yanzu.

Daga nan ne Mai Shari’a, Ekwo ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 21 ga watan Fabrarirun 2022 domin yanke hukunci.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp