fidelitybank

Siyasa: Atiku zai san matsayin sa na tsayawa takara a sabuwar shekara

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta sanya ranar 21 ga watan Fabrairun 2022, domin yanke hukunci kan ko tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya cancanci tsayawa takarar shugaban Kasa ko a’a.

Mai Shari’a, Inyang Ekwo ne ya sanya ranar da hakan a ranar Litinin, bayan kammala sauraron muhawara tsakanin lauyoyin bangarorin Biyu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa wani kamfani mai zaman kansa mai suna EMA ne ya maka Atikun da jam’iyyar PDP da hukumar zabe (INEC) da kuma Babban Lauyan gwamnatin tarayya a gaban kotun.

Kamfanin dai na kalubalantar cancantar Atikun ta tsayawa takarar shugaban kasa, bisa hujjar cewa ba asalin dan Najeriya ba ne ta nasabar haihuwa.

Ya roki kotun da ta yi la’akari da tande-tanaden sashi na 25 Daya cikin baka (1) da Biyu cikin baka (2) da kuma 131 (a) na kundin tsarin mulki wajen hana shi takarar.

A baya dai gwamnatin jihar Adamawa ta roki kotun da ta saka ta cikin wadanda ake tafka shari’ar da su, inda a ranar 27 ga watan Yulin 2021 kotun ta maince da hakan.

Jihar dai ta shaida wa kotun cewa Atikun ya cancanci tsayawa takara, kuma har ya taba jagorantar Jihar da kuma zama mataimakin shugaban kasa na tsawon shekara Takwas.

To sai dai lauyan masu kara, Oladimeji ya ce ko da ya ke a Najeriya aka haifi Atiku, hakan ba yana nufin shi dan Najeriya ba ne.

A cewarsa, kasancewar an yi kuskure a baya, ba ya nufin a sake maimaita hakan a yanzu.

Daga nan ne Mai Shari’a, Ekwo ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 21 ga watan Fabrarirun 2022 domin yanke hukunci.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp