Kungiyar Malaman Jami’a (ASUU) ta ce za ta dauki matakin da ya dace nan da kwanaki biyu masu zuwa a kan gwamnatin tarayya, saboda gazawar gwamnatin ta cika alkawuran da ta yi mata.
Shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ne, ya bayyana haka a tattaunawarsa da Aminiya a ranar Litinin ta wayar tarho.
Shugaban kungiyar ya ce”Za su zartar da hukuncin da ya dace a ranar Talata tare da sanar da dukkanin sauran mambobinta matsayarta game da gwamnatin tarayya”. Inji Farfesa Emmanuel.
Idan ba a manta ba, a ranar 14 ga watan Oktoba ne ASUU da Ministan Kwadago, Chris Ngige suka gana tare da tattaunawa kan cika alkawuran da gwamnatin tarayya ta daukar musu.
Daga cikin matsalolin da suka tattauna akwai bukatar yih gyare-gyare a wasu jami’o’in kasar nan da kuma biyan alawus din malamai.
Kazalika, an tattauna wasu alkawura da aka yi wa kungiyar tun a shekarar 2009 da kuma tsarin biyan albashin ma’aikata na IPPIS da kungiyar take adawa da shi.