fidelitybank

Garkuwa da Mutane: Jami’ar Abuja ta dauki ‘yan sintiri da ‘yan Banga da mafarauta

Date:

Jami’ar Abuja ta kaddamar da aikin sintiri na awa 24 a cikin harabarta da kewaya ta hanyar amfani da mafarauta da ’yan banga, domin dakile ayyukan ’yan bindiga.

Uban Jami’ar Abuja, Modibbo Mohammed, ya ce an dauki matakin ne bayan harin ’yan bindiga da suka yi garkuwa da wasu ma’aikata a rukunin gidajensu da ke cikin jami’ar.

Ya ce,“Mun dauki mafarauta da ’yan banga su rika gudanar da sintiri a yankin da babu Katanga, saboda filin jami’ar na da girma sosai,” inji shi.

Amiya ta rawaito cewa, Uban Jami’ar Abuja ya shaida wa taron manyan shugabanni da jami’an gudanarwa da na kungiyoyin jami’ar, cewa su na yin duk mai yiwuwa, domin ganin ba a sake kai hari ba a jami’ar.

Da ya ke magana game da halin da gidajen ma’aikatan jami’ar su ke ciki, ya ce, “Gidajen ma’aikatan mu ba su kai yadda ake bukata ba, har kunya na ke ji game da irin gidajen da ma’aikatanmu ke zaune a ciki. Kwamitin gudanarwar Jami’ar ya yi zama da Ministan Abuja a kan lamarin, kuma ministan ya yi alkawarin daukar mataki a kai, nan ba da jimawa ba. Nan gaba kadan kuma za mu tura wakilanmu zuwa hukumar FERMA, domin ta bayar da muhimmanci wajen gyara hanyoyin da ke cikin jami’ar,” inji Modibo.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp