fidelitybank

Rikicin Siyasa: Zaben wakilai a jam’iyar PDP ya bar baya da kura a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bangar siyasa sun mamaye harabar jam’iyyar PDP a jihar Zamfara, sa’o’i kadan kafin a fara gudanar da zabe wakilai.

Shirin da a ka shirya tun farko na kamfanin man Zaitun dake bayan hukumar alhazai ta jihar, an mayar da shi gidan baki na Command da ke Gusau babban birnin jihar.

A cewar gidan talabijin na Channels, ‘yan barandan sun kai farmaki wurin ne da sanyin safiyar ranar Litinin, inda su ka lalata kayayyakin zabe da fom din tsayawa takara da motoci biyu na ‘yan jam’iyyar tare da kujeru.

Babban Sakataren mataimakin gwamnan Jihar Zamfara, Umar Aminu, ya ce, lamarin ba zai yi wa jam’iyyar barazana ba, ya na mai cewa taron zai gudana kamar yadda a ka tsara.

Ya ce,”Har yanzu ba a san ko su waye ba, kuma na tabbatar da cewa jami’an tsaro za su yi bincike a kai. Ba a dai san ko wace jam’iyya ce ke da alhakin harin da a ka kai a taron jam’iyyar PDP a jihar Arewa maso Yammacin kasar.

Yadda a ka faffasa kujeru tare da kona rumfar zabe a taron PDP

Duk da harin, mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mahdi Gusau da shugaban riko na jam’iyyar Ambasada Bala Mande sun isa sabon wurin taron.

Zaben wakilan kimanin 1,089 wanda za a gudanar da shi da nufin samar da manyan jami’an PDP wadanda za su gudanar da harkokin jam’iyyar.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...
X whatsapp