Wasu ‘yan bangar siyasa sun mamaye harabar jam’iyyar PDP a jihar Zamfara, sa’o’i kadan kafin a fara gudanar da zabe wakilai.
Shirin da a ka shirya tun farko na kamfanin man Zaitun dake bayan hukumar alhazai ta jihar, an mayar da shi gidan baki na Command da ke Gusau babban birnin jihar.
A cewar gidan talabijin na Channels, ‘yan barandan sun kai farmaki wurin ne da sanyin safiyar ranar Litinin, inda su ka lalata kayayyakin zabe da fom din tsayawa takara da motoci biyu na ‘yan jam’iyyar tare da kujeru.
Babban Sakataren mataimakin gwamnan Jihar Zamfara, Umar Aminu, ya ce, lamarin ba zai yi wa jam’iyyar barazana ba, ya na mai cewa taron zai gudana kamar yadda a ka tsara.
Ya ce,”Har yanzu ba a san ko su waye ba, kuma na tabbatar da cewa jami’an tsaro za su yi bincike a kai. Ba a dai san ko wace jam’iyya ce ke da alhakin harin da a ka kai a taron jam’iyyar PDP a jihar Arewa maso Yammacin kasar.

Duk da harin, mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mahdi Gusau da shugaban riko na jam’iyyar Ambasada Bala Mande sun isa sabon wurin taron.
Zaben wakilan kimanin 1,089 wanda za a gudanar da shi da nufin samar da manyan jami’an PDP wadanda za su gudanar da harkokin jam’iyyar.