fidelitybank

Rashe-rashen da a ka yi wa Kano mutane ne jajirtattu – Kungiyar Dattawan Arewa

Date:

Kungiyar Dattawan Arewa (N.E.F) ta yi wa gwamnatin jihar Kano ta’aziyyar rasuwar wasu jiga-jigan ‘ya’yanta ’yan Jihar Kano da su ka koma ga mahalicci.

A yayin da ya ke jagorantar tawagar, shugaban Kungiyar, Farfesa Ango Abdullahi, wanda Wazirin Bauchi Alh.Muhammad Bello Kirfi ya wakilta, ya ce, sun zo gidan gwamnatin Kano ne, domin mika ta’aziyyar rasuwar wasu dattijan jihar da suka rasu kwanan nan.

“Mun zo nan ne, domin ta’aziyyar rasuwar Sarkin Bai, Alh.Muktar Adnan wanda mutum ne mai daraja, da kuma babban likita wanda a ka assasa Wannan kungiyar da shi, Dr. Ibrahim Datti Ahmad da kuma cikakken dan siyasa, Alh.Bashir Othman Tofa.”

“Sarkin Bai uba ne a gare mu, Dr.Ibrahim Datti Ahmad ya kasance mai himma a dukkan ayyukanmu yayin da Alh.Bashir Tofa ya kasance mai hangen nesa da kishin kasa domi son ci gaban al’umma”. inji Ango Abdullahi.

“Wadannan jiga-jigan mutane sun taimaka matuka gaya wajen ci gaban Arewacin Najeriya da ma kasa baki daya.

Ya kara da cewa suna alhinin rasuwar wadannan manyan mutane wadanda suka bada gudumawa tare da yin tasiri ga ci gaban bil’adama a kasar nan baki daya.

 “Za mu ci gaba da addu’ar Allah Ta’ala ya gafarta musu ya karbi ayyukansu na alheri ya kuma ba su Jannatul Firdaus ya kuma baiwa jihar da iyalansu hakuri jure rashin su”. Inji Ango Abdullahi

Farfesa Ango ya kuma yabawa gwamnatin jihar Kano bisa wannan tarba da a ka yi musu.

Cikin wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran mataimakin gGwamna, Hassan Musa fagge wanda ya rabawa manema labarai ya ce da ya ke mayar da Jawabi, gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana jin dadinsa bisa ga ziyarar ta’aziyya da Kungiyar Dattawan Arewa ta kawo wa gwamnati da al’ummar Jihar Kano.

“Hakika mun rasa wasu dattijai wadanda basu da son kansu sun bayar da gudunmawa sosai wajen cigaban jihar Kano da Kasa baki daya”. Inji Dr Gawuna

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...
X whatsapp