fidelitybank

Rashe-rashen da a ka yi wa Kano mutane ne jajirtattu – Kungiyar Dattawan Arewa

Date:

Kungiyar Dattawan Arewa (N.E.F) ta yi wa gwamnatin jihar Kano ta’aziyyar rasuwar wasu jiga-jigan ‘ya’yanta ’yan Jihar Kano da su ka koma ga mahalicci.

A yayin da ya ke jagorantar tawagar, shugaban Kungiyar, Farfesa Ango Abdullahi, wanda Wazirin Bauchi Alh.Muhammad Bello Kirfi ya wakilta, ya ce, sun zo gidan gwamnatin Kano ne, domin mika ta’aziyyar rasuwar wasu dattijan jihar da suka rasu kwanan nan.

“Mun zo nan ne, domin ta’aziyyar rasuwar Sarkin Bai, Alh.Muktar Adnan wanda mutum ne mai daraja, da kuma babban likita wanda a ka assasa Wannan kungiyar da shi, Dr. Ibrahim Datti Ahmad da kuma cikakken dan siyasa, Alh.Bashir Othman Tofa.”

“Sarkin Bai uba ne a gare mu, Dr.Ibrahim Datti Ahmad ya kasance mai himma a dukkan ayyukanmu yayin da Alh.Bashir Tofa ya kasance mai hangen nesa da kishin kasa domi son ci gaban al’umma”. inji Ango Abdullahi.

“Wadannan jiga-jigan mutane sun taimaka matuka gaya wajen ci gaban Arewacin Najeriya da ma kasa baki daya.

Ya kara da cewa suna alhinin rasuwar wadannan manyan mutane wadanda suka bada gudumawa tare da yin tasiri ga ci gaban bil’adama a kasar nan baki daya.

 “Za mu ci gaba da addu’ar Allah Ta’ala ya gafarta musu ya karbi ayyukansu na alheri ya kuma ba su Jannatul Firdaus ya kuma baiwa jihar da iyalansu hakuri jure rashin su”. Inji Ango Abdullahi

Farfesa Ango ya kuma yabawa gwamnatin jihar Kano bisa wannan tarba da a ka yi musu.

Cikin wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran mataimakin gGwamna, Hassan Musa fagge wanda ya rabawa manema labarai ya ce da ya ke mayar da Jawabi, gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana jin dadinsa bisa ga ziyarar ta’aziyya da Kungiyar Dattawan Arewa ta kawo wa gwamnati da al’ummar Jihar Kano.

“Hakika mun rasa wasu dattijai wadanda basu da son kansu sun bayar da gudunmawa sosai wajen cigaban jihar Kano da Kasa baki daya”. Inji Dr Gawuna

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp