fidelitybank

Rashe-rashen da a ka yi wa Kano mutane ne jajirtattu – Kungiyar Dattawan Arewa

Date:

Kungiyar Dattawan Arewa (N.E.F) ta yi wa gwamnatin jihar Kano ta’aziyyar rasuwar wasu jiga-jigan ‘ya’yanta ’yan Jihar Kano da su ka koma ga mahalicci.

A yayin da ya ke jagorantar tawagar, shugaban Kungiyar, Farfesa Ango Abdullahi, wanda Wazirin Bauchi Alh.Muhammad Bello Kirfi ya wakilta, ya ce, sun zo gidan gwamnatin Kano ne, domin mika ta’aziyyar rasuwar wasu dattijan jihar da suka rasu kwanan nan.

“Mun zo nan ne, domin ta’aziyyar rasuwar Sarkin Bai, Alh.Muktar Adnan wanda mutum ne mai daraja, da kuma babban likita wanda a ka assasa Wannan kungiyar da shi, Dr. Ibrahim Datti Ahmad da kuma cikakken dan siyasa, Alh.Bashir Othman Tofa.”

“Sarkin Bai uba ne a gare mu, Dr.Ibrahim Datti Ahmad ya kasance mai himma a dukkan ayyukanmu yayin da Alh.Bashir Tofa ya kasance mai hangen nesa da kishin kasa domi son ci gaban al’umma”. inji Ango Abdullahi.

“Wadannan jiga-jigan mutane sun taimaka matuka gaya wajen ci gaban Arewacin Najeriya da ma kasa baki daya.

Ya kara da cewa suna alhinin rasuwar wadannan manyan mutane wadanda suka bada gudumawa tare da yin tasiri ga ci gaban bil’adama a kasar nan baki daya.

 “Za mu ci gaba da addu’ar Allah Ta’ala ya gafarta musu ya karbi ayyukansu na alheri ya kuma ba su Jannatul Firdaus ya kuma baiwa jihar da iyalansu hakuri jure rashin su”. Inji Ango Abdullahi

Farfesa Ango ya kuma yabawa gwamnatin jihar Kano bisa wannan tarba da a ka yi musu.

Cikin wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran mataimakin gGwamna, Hassan Musa fagge wanda ya rabawa manema labarai ya ce da ya ke mayar da Jawabi, gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana jin dadinsa bisa ga ziyarar ta’aziyya da Kungiyar Dattawan Arewa ta kawo wa gwamnati da al’ummar Jihar Kano.

“Hakika mun rasa wasu dattijai wadanda basu da son kansu sun bayar da gudunmawa sosai wajen cigaban jihar Kano da Kasa baki daya”. Inji Dr Gawuna

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp