fidelitybank

Kano Pillars za ta dawo Kano wasa nan ba da jimawa ba – Lakwaya

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta gina wa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars sansanin ‘yan wasa da sakatariya.

Kwamishinan matasa da cigaban harkokin wasannnin na jahar Kano, Kwamrade Kabir Ado Lakwaya ya tabbatar da hakan yayin bude babban taron masu ruwa da tsaki na hukumar wasan kwallon kafa ta jahar Kano na shekara ta 2021.

Ya ce”Za a gina sansanin ‘yan wasan ne da za su rinka kasance wuri guda da sakatariyar a tsohuwar tashar manyan motoci da ke kan titin New road a unguwar sabon gari.

Ya kuma ce”Shirye-shirye sun yi nisa, domin samar da kayayyakin wasanni ga kungiyoyi sama da dubu biyu a Kano”.

Lakwaya ya kara da cewa,”Gwamnatin jihar ta na yin kokarin ganin an samar da sabuwar ciyawa a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata, domin ganin nan ba dadewa ba kungiyar Kano Pillars ta dawo gida Kano da buga wasannin ta na gasar Premier ta kasa, maimakon yadda ta ke buga wasannin ta a jihar Kaduna”.

Lakwaya ya kuma yabawa hukumar wasanni kwallon kafa ta jihar Kano karkashin jagorancin, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, bisa yadda ta ke kokari wajen samar da ci gaban harkokin wasannnin kwallon kafa a jihar da kuma hade kan masu ruwa da tsaki a kan wasanni kwallon kafa wuri guda.

A nasa bangaren shugaban hukumar kwallon kafa ta jihar Kano, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, ya godewa gwamnatin jihar, bisa kulawar da ta ke baiwa harkokin wasannni.

Ya kuma ce taron ya tattauna kan yadda za a gudanar da zabuka a matakan kwamitocin kanan hukumomi.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp