fidelitybank

Ramuwar Gayya: Bururruka sun kashe Karnuka 250

Date:

Wasu tarin Bururruka a wani birnin Indiya sun kashe karnuka 250, tare da jefo su daga saman manyan gine-gine da bishiyoyi.

Kafar labarai ta News18 ta rawaito cewa, mazauna yankin Labool, wani gari ne mai kimanin mutum 5,000 da ke da nisan mil 300 a Gabas da birnin Mumbai, sun shaida wa News18 cewa, Birrai sun fara daukar fansa ne a watan jiya bayan da wasu karnuka su ka kashe wani dan biri.

Mazauna yankin sun ce tun daga lokacin ne birrai su ka fara farautar karnuka ta yadda da zarar sun hango su sai su ja su zuwa saman dogayen gine-gine ko bishiyoyin suna jefo su kasa har lahira.

Kafar labarai ta Newsweek ta rawaito cewa, kusan kowane Kare a garin an kashe shi.

Newsweek ta ce, an kira jami’ai daga Sashen Kula da Dazuzzuka a yankin, domin su taimaka wajen kama Birran, amma ba su iya kama ko daya ba. Daga nan ne mazauna kauyukan su ka yi kokarin kama su.

News18, ta ce, da yawa daga cikin Birran sun samu raunuka a kokarin kisan karnukan.

“Birrai a yanzu suna kai hari kan kananan karnuka, suna haifar da ‘firgici’ a yankin Labool,” kamar yadda News 18 ta rawaito.

Mataimakin Farfesa a Jami’ar SUNY Buffalo, Stephanie Poindedter, wanda bincikensa ya mayar da hankali a kan halayyar halittu wadanda suke da tafin hannu, tafin kafa da kuma fuska mai dauke da idanu da suke fuska kamar dan Adam da birrai, ya ce, “A cikin binciken da aka yi game da irin wadannan halittu da ake killacewa, a cikin wuraren da jama’a ke ziyarta kamar gidajen namun daji, mun gano cewa lokacin da aka kai wa irin halittun hari ta wata hanya, akwai yiwuwar su mai da martani ta hanyar kai hari ga wanda ke da alaka da wanda ya zalunce su, kuma martanin zai fi tsanani fiye da yadda aka kai masu”. A cewar Dailytrust.

 

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp