fidelitybank

Ramuwar Gayya: Bururruka sun kashe Karnuka 250

Date:

Wasu tarin Bururruka a wani birnin Indiya sun kashe karnuka 250, tare da jefo su daga saman manyan gine-gine da bishiyoyi.

Kafar labarai ta News18 ta rawaito cewa, mazauna yankin Labool, wani gari ne mai kimanin mutum 5,000 da ke da nisan mil 300 a Gabas da birnin Mumbai, sun shaida wa News18 cewa, Birrai sun fara daukar fansa ne a watan jiya bayan da wasu karnuka su ka kashe wani dan biri.

Mazauna yankin sun ce tun daga lokacin ne birrai su ka fara farautar karnuka ta yadda da zarar sun hango su sai su ja su zuwa saman dogayen gine-gine ko bishiyoyin suna jefo su kasa har lahira.

Kafar labarai ta Newsweek ta rawaito cewa, kusan kowane Kare a garin an kashe shi.

Newsweek ta ce, an kira jami’ai daga Sashen Kula da Dazuzzuka a yankin, domin su taimaka wajen kama Birran, amma ba su iya kama ko daya ba. Daga nan ne mazauna kauyukan su ka yi kokarin kama su.

News18, ta ce, da yawa daga cikin Birran sun samu raunuka a kokarin kisan karnukan.

“Birrai a yanzu suna kai hari kan kananan karnuka, suna haifar da ‘firgici’ a yankin Labool,” kamar yadda News 18 ta rawaito.

Mataimakin Farfesa a Jami’ar SUNY Buffalo, Stephanie Poindedter, wanda bincikensa ya mayar da hankali a kan halayyar halittu wadanda suke da tafin hannu, tafin kafa da kuma fuska mai dauke da idanu da suke fuska kamar dan Adam da birrai, ya ce, “A cikin binciken da aka yi game da irin wadannan halittu da ake killacewa, a cikin wuraren da jama’a ke ziyarta kamar gidajen namun daji, mun gano cewa lokacin da aka kai wa irin halittun hari ta wata hanya, akwai yiwuwar su mai da martani ta hanyar kai hari ga wanda ke da alaka da wanda ya zalunce su, kuma martanin zai fi tsanani fiye da yadda aka kai masu”. A cewar Dailytrust.

 

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp