fidelitybank

Omicron:  Mutum 45 sun kamu da cutar a Najeriya – NCDC

Date:

A jiya ne Cibiyar Kula da Cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta sanar da cewa kawo yanzu an samu bullar cutar guda 45 na Omicron na COVID-19 a kasar nan, ba tare da an samu mace-mace ba.

Darakta-Janar na NCDC, Dr Ifedayo Adetifa, wanda ya bayyana kididdigar Omicron ta Najeriya a wani taron manema labarai, ya ce, sabbin kwayoyin cutar sun kasance a cikin mutanen da ba su da tarihin tafiya, wanda ke nuna cewa kasar ta riga ta fara kamuwa da cutar.

Adetifa ya ce”Mutane Shida na Omicron da a ka gano a baya su na cikin mutanen da ke da tarihin balaguro zuwa Afirka ta Kudu, ya na da kyau ‘yan Najeriya su kiyaye tazarar jiki tare da kaucewa cudanya da duk wanda ke nuna alamun cutar numfashi”.

Ya kara da cewa “Muna dogaro da ku kare kanku da masoyinka daga COVID-19,” inji shi.

Adetifa ya kuma shawarci ‘yan Najeriya da su kara bin matakan da za su iya dakile yaduwar Omicron kamar su rage yawan taro, kara nisantar jiki, tsawon lokacin saduwa da kuma yiwuwar rufe wuraren da a ke ganin suna da hadari sosai.

Adetifa ya bukaci ‘yan Najeriya da su dauki shawarar da kwamitin shugaban kasa ya bayar kan COVID-19 da muhimmanci, ya kara da cewa hakan zai kara habaka tasirin irin wadannan ayyukan.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp