fidelitybank

Gasar Kwalliya: Shatu Garko ta mayar da martani a kan kambun ta

Date:

Wacce ta lashe gasar Miss Nigeria gasar kwalliya ta mata kyau ta 2021, Shatu Garko, ta mayar da martani kan sukar da a ka yi mata game da halartar gasar kwalliya ta bana.

A kwanan baya Garko, wadda ‘yar Kano ce, ta zama ‘yar takara na farko da ta fara sanye da hijabi da ta lashe kambun da a ke so tun bayan da a ka fara gasar a shekarar 1957.

Duk da haka, kasancewarta a gasar ta ci gaba da haifar da cece-kuce, saboda addininta na Musulunci.

Da ta ke magana a wata hira da BBC Pidgin, matashiyar mai shekaru 18 ta caccaki masu sukan ta ta na mai cewa “Yan Najeriya na son yanke hukunci da kan su”. A cewar Shatu Garko.

Sabuwar Miss Nigeria ta kuma musanta ikirarin da wasu mutane ke yi na cewa ta biya, domin ta zama zakara a gasar.

“Gaskiya ’yan Najeriya suna son yin hukunci a kan mutane. Jama’a da dama sun ce shugaban kasa ne ya biya ni domin in samu rawanin, wasu kuma sun ce gwamnan jihar ya biya ya bani rawani. Akwai kuma wadanda su ka ce iyayena sun biya Miss Nigeria, amma hakan ba gaskiya ba ne,” inji ta.

Da ta ke magana kan ikirarin Hisbah, Garko ta bayyana cewa har yanzu ba a gayyace ta ba, amma ta sha samun kalamai masu zafi daga mutane.

Sai dai samfurin hijabi, ta bayyana cewa har yanzu ba ta damu da sukar da a ke mata ba, ta kara da cewa babu wani abu da za ta iya yi game da kambun.

“Babu wanda ya kira ni amma na sami maganganu da yawa da cewa ‘Na kasance tsirara’, ‘Ina yin abin da bai dace ba,” inji Shatu.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp