fidelitybank

Matashi ya ƙona mahaifiyarsa ta rasu a Naija

Date:

 

Mazauna unguwar Darusalam da ke Minna, Jihar Naija sun tashi cikin kaɗuwa da firgici bayan da wani matashi, mai suna Steven Jiya, ya bankawa mahaifiyarsa, Comfort Jiya wuta.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa a ranar Litinin ɗin da ta gabata ne dai Steven, wanda ɗan ƙwaya ne, ya dawo da ga garin Suleja a Jihar Naija ɗin dai, inda bayan ya dawo gida ne, sai kawai ta raya masa cewa ya ƙona mahaifiyarsa.
Jaridar ta ce a lokacin Comfort, wacce tsohuwar Shugabar makarantar sakandire ce, tana tsaka da girki a kicin, sai kawai wannan tambaɗaɗɗen ɗa ya zazzaga mata fetur ya kuma cinna mata wuta a gidanta da ke unguwar Darusalam ya kuma tsere.
Nan fa ta fito a waje tana ihu a kawo mata ɗauki, inda kan ka ce kwabo, wutar ta ƙone mata ilahirin jikinta.
Wata majiya a dangin marigayiyar ta ce an garzaya da ita asibiti inda ta ke jiyya.
Sai dai kuma, da misalin ƙarfe 3  na yammacin jiya Juma’a, marigayiya Comfort ta ce ga garin ku nan.
Wata majiyar ta ƙara da cewa dama can Steven fitinanne ne kuma ya yi yunƙurin hallaka uwar tun a baya.
Jaridar ta ce ta tuntuɓi rundunar ƴan sanda ta Naija amma haƙar ta ba ta cimma ruwa ba.
Sai dai kuma, in ji jaridar, tuni dai ƴan sandan Caji-ofis na Minna su ka samu nasarar damƙe Steven kuma har an kai shi babbar kotun Minna inda zai girbe abin da ya shuka.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp