fidelitybank

Matashi ya ƙona mahaifiyarsa ta rasu a Naija

Date:

 

Mazauna unguwar Darusalam da ke Minna, Jihar Naija sun tashi cikin kaɗuwa da firgici bayan da wani matashi, mai suna Steven Jiya, ya bankawa mahaifiyarsa, Comfort Jiya wuta.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa a ranar Litinin ɗin da ta gabata ne dai Steven, wanda ɗan ƙwaya ne, ya dawo da ga garin Suleja a Jihar Naija ɗin dai, inda bayan ya dawo gida ne, sai kawai ta raya masa cewa ya ƙona mahaifiyarsa.
Jaridar ta ce a lokacin Comfort, wacce tsohuwar Shugabar makarantar sakandire ce, tana tsaka da girki a kicin, sai kawai wannan tambaɗaɗɗen ɗa ya zazzaga mata fetur ya kuma cinna mata wuta a gidanta da ke unguwar Darusalam ya kuma tsere.
Nan fa ta fito a waje tana ihu a kawo mata ɗauki, inda kan ka ce kwabo, wutar ta ƙone mata ilahirin jikinta.
Wata majiya a dangin marigayiyar ta ce an garzaya da ita asibiti inda ta ke jiyya.
Sai dai kuma, da misalin ƙarfe 3  na yammacin jiya Juma’a, marigayiya Comfort ta ce ga garin ku nan.
Wata majiyar ta ƙara da cewa dama can Steven fitinanne ne kuma ya yi yunƙurin hallaka uwar tun a baya.
Jaridar ta ce ta tuntuɓi rundunar ƴan sanda ta Naija amma haƙar ta ba ta cimma ruwa ba.
Sai dai kuma, in ji jaridar, tuni dai ƴan sandan Caji-ofis na Minna su ka samu nasarar damƙe Steven kuma har an kai shi babbar kotun Minna inda zai girbe abin da ya shuka.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa ƴar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar Ɗangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp