fidelitybank

Matashi ya ƙona mahaifiyarsa ta rasu a Naija

Date:

 

Mazauna unguwar Darusalam da ke Minna, Jihar Naija sun tashi cikin kaɗuwa da firgici bayan da wani matashi, mai suna Steven Jiya, ya bankawa mahaifiyarsa, Comfort Jiya wuta.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa a ranar Litinin ɗin da ta gabata ne dai Steven, wanda ɗan ƙwaya ne, ya dawo da ga garin Suleja a Jihar Naija ɗin dai, inda bayan ya dawo gida ne, sai kawai ta raya masa cewa ya ƙona mahaifiyarsa.
Jaridar ta ce a lokacin Comfort, wacce tsohuwar Shugabar makarantar sakandire ce, tana tsaka da girki a kicin, sai kawai wannan tambaɗaɗɗen ɗa ya zazzaga mata fetur ya kuma cinna mata wuta a gidanta da ke unguwar Darusalam ya kuma tsere.
Nan fa ta fito a waje tana ihu a kawo mata ɗauki, inda kan ka ce kwabo, wutar ta ƙone mata ilahirin jikinta.
Wata majiya a dangin marigayiyar ta ce an garzaya da ita asibiti inda ta ke jiyya.
Sai dai kuma, da misalin ƙarfe 3  na yammacin jiya Juma’a, marigayiya Comfort ta ce ga garin ku nan.
Wata majiyar ta ƙara da cewa dama can Steven fitinanne ne kuma ya yi yunƙurin hallaka uwar tun a baya.
Jaridar ta ce ta tuntuɓi rundunar ƴan sanda ta Naija amma haƙar ta ba ta cimma ruwa ba.
Sai dai kuma, in ji jaridar, tuni dai ƴan sandan Caji-ofis na Minna su ka samu nasarar damƙe Steven kuma har an kai shi babbar kotun Minna inda zai girbe abin da ya shuka.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp