fidelitybank

Majalisun tarayya da jihohi da na kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946

Date:

Ma’aikatar kudi da kasafi da tsare-tsare ta bayyana cewa majalisun tarayya da na jihohi da kuma kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946 daga asusun tarayya na watan Nuwamba a ranar Juma’a.

Olajide Oshundun, mukaddashin daraktan yada labarai na ma’aikatar kudi, kasafin kudi da tsare-tsare ta kasa ne ya bayyan hakan ranar Asabar a Abuja.

Gwamnatin tarayya ta karbi Naira biliyan 261.441 na kudaden, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 210.046 da kuma Naira biliyan 155.456.

Jihohin da su ke hako mai sun samu karin Naira biliyan 49.003 a matsayin kashi 13 na asusun rarar man.

Jimlar kudaden shiga na VAT da a ka tara a watan Nuwamba ya kai Naira biliyan 196.175 sabanin Naira biliyan 166.284 a watan Oktoba, wanda ya nuna an samu karin Naira biliyan 29.891.

Daga kudaden shiga na VAT, gwamnatin tarayya ta samu Naira biliyan 27.402, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 91.339, da kuma Naira biliyan 63.937.

Hukumar tara kudaden shiga ta tarayya da hukumar kwastam ta Najeriya da hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya ta samu Naira biliyan 7.847 a matsayin kudin tattara kudaden shiga yayin da aikin hukumar raya yankin arewa maso gabas ya samu Naira biliyan 5.650.

Oshundun ya bayyana cewar, rabon kudaden shigar an gudanar da shi ne a wani a taron kwamitin raba asusun ajiya na tarayya wanda babban sakatare a ma’aikatar Mista Aliyu Ahmed ya jagoranta.

 

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...
X whatsapp