fidelitybank

Majalisun tarayya da jihohi da na kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946

Date:

Ma’aikatar kudi da kasafi da tsare-tsare ta bayyana cewa majalisun tarayya da na jihohi da kuma kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946 daga asusun tarayya na watan Nuwamba a ranar Juma’a.

Olajide Oshundun, mukaddashin daraktan yada labarai na ma’aikatar kudi, kasafin kudi da tsare-tsare ta kasa ne ya bayyan hakan ranar Asabar a Abuja.

Gwamnatin tarayya ta karbi Naira biliyan 261.441 na kudaden, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 210.046 da kuma Naira biliyan 155.456.

Jihohin da su ke hako mai sun samu karin Naira biliyan 49.003 a matsayin kashi 13 na asusun rarar man.

Jimlar kudaden shiga na VAT da a ka tara a watan Nuwamba ya kai Naira biliyan 196.175 sabanin Naira biliyan 166.284 a watan Oktoba, wanda ya nuna an samu karin Naira biliyan 29.891.

Daga kudaden shiga na VAT, gwamnatin tarayya ta samu Naira biliyan 27.402, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 91.339, da kuma Naira biliyan 63.937.

Hukumar tara kudaden shiga ta tarayya da hukumar kwastam ta Najeriya da hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya ta samu Naira biliyan 7.847 a matsayin kudin tattara kudaden shiga yayin da aikin hukumar raya yankin arewa maso gabas ya samu Naira biliyan 5.650.

Oshundun ya bayyana cewar, rabon kudaden shigar an gudanar da shi ne a wani a taron kwamitin raba asusun ajiya na tarayya wanda babban sakatare a ma’aikatar Mista Aliyu Ahmed ya jagoranta.

 

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp