fidelitybank

Majalisun tarayya da jihohi da na kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946

Date:

Ma’aikatar kudi da kasafi da tsare-tsare ta bayyana cewa majalisun tarayya da na jihohi da kuma kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946 daga asusun tarayya na watan Nuwamba a ranar Juma’a.

Olajide Oshundun, mukaddashin daraktan yada labarai na ma’aikatar kudi, kasafin kudi da tsare-tsare ta kasa ne ya bayyan hakan ranar Asabar a Abuja.

Gwamnatin tarayya ta karbi Naira biliyan 261.441 na kudaden, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 210.046 da kuma Naira biliyan 155.456.

Jihohin da su ke hako mai sun samu karin Naira biliyan 49.003 a matsayin kashi 13 na asusun rarar man.

Jimlar kudaden shiga na VAT da a ka tara a watan Nuwamba ya kai Naira biliyan 196.175 sabanin Naira biliyan 166.284 a watan Oktoba, wanda ya nuna an samu karin Naira biliyan 29.891.

Daga kudaden shiga na VAT, gwamnatin tarayya ta samu Naira biliyan 27.402, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 91.339, da kuma Naira biliyan 63.937.

Hukumar tara kudaden shiga ta tarayya da hukumar kwastam ta Najeriya da hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya ta samu Naira biliyan 7.847 a matsayin kudin tattara kudaden shiga yayin da aikin hukumar raya yankin arewa maso gabas ya samu Naira biliyan 5.650.

Oshundun ya bayyana cewar, rabon kudaden shigar an gudanar da shi ne a wani a taron kwamitin raba asusun ajiya na tarayya wanda babban sakatare a ma’aikatar Mista Aliyu Ahmed ya jagoranta.

 

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp