fidelitybank

Majalisun tarayya da jihohi da na kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946

Date:

Ma’aikatar kudi da kasafi da tsare-tsare ta bayyana cewa majalisun tarayya da na jihohi da kuma kananan hukumomi sun raba Naira biliyan 675.946 daga asusun tarayya na watan Nuwamba a ranar Juma’a.

Olajide Oshundun, mukaddashin daraktan yada labarai na ma’aikatar kudi, kasafin kudi da tsare-tsare ta kasa ne ya bayyan hakan ranar Asabar a Abuja.

Gwamnatin tarayya ta karbi Naira biliyan 261.441 na kudaden, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 210.046 da kuma Naira biliyan 155.456.

Jihohin da su ke hako mai sun samu karin Naira biliyan 49.003 a matsayin kashi 13 na asusun rarar man.

Jimlar kudaden shiga na VAT da a ka tara a watan Nuwamba ya kai Naira biliyan 196.175 sabanin Naira biliyan 166.284 a watan Oktoba, wanda ya nuna an samu karin Naira biliyan 29.891.

Daga kudaden shiga na VAT, gwamnatin tarayya ta samu Naira biliyan 27.402, yayin da jihohi da kananan hukumomi suka samu Naira biliyan 91.339, da kuma Naira biliyan 63.937.

Hukumar tara kudaden shiga ta tarayya da hukumar kwastam ta Najeriya da hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya ta samu Naira biliyan 7.847 a matsayin kudin tattara kudaden shiga yayin da aikin hukumar raya yankin arewa maso gabas ya samu Naira biliyan 5.650.

Oshundun ya bayyana cewar, rabon kudaden shigar an gudanar da shi ne a wani a taron kwamitin raba asusun ajiya na tarayya wanda babban sakatare a ma’aikatar Mista Aliyu Ahmed ya jagoranta.

 

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp