Wata budurwa ‘yar shekara 18, mai suna Shatu Garko, ‘yar asalin jihar Kano, ta zama mace ta 44 a Najeriya da ta fi kowa iya kwalliya.
Shatu Garko ta kasance mai sanye da hijabi kafin a ba ta sarautar Miss Najeriya.
An zabo mutane 37 da suka fito daga jihohin Najeriya daban-daban a matakin farko na gasar. Daga nan ne kuma a ka zabi wasu manyan mutane 18 da su ka fafata a gasar Miss Najeriya ta 44 da za su fafata a ranar karshe da ta kasance daren Juma’a.
Garko ta kai matsayi na Takwas a matsayin wanda da fito daga yankin Arewa maso Yamma, tare da sauran mahalarta Bakwai.
A yayin da Miss Najeriya ta 44, Garko ta samu kyautar Naira miliyan 10 da sabuwar mota kuma za ta zauna na shekara 1 a wani katafaren gida.