fidelitybank

Majalisar Dattijai da Wakilai: An bankado badakalar Naira biliyan 8.5

Date:

Ofishin binciken kudi na tarayya ya bankado badakalar Naira biliyan 8.5 a zaurukan majalisar dokoki ta tarayya.

Rahoton binciken kudin ya gano yadda shugabancin zaurukan biyu suka kashe Naira biliyan Uku a majalisar dattawa da wasu biliyan 5.5 a majalisar wakilai a shekarar 2019 ba tare da shaidar kashe kudaden ba.

Mai binciken kudi na tarayya, Aghughu Adolphus, a rahoton sa, ya bankado yadda majalisar dattawa da majalisar wakilai da hukumar kula da harkokin majalisar dokoki ta kasa suka kashe kudaden ba bisa ka’ida ba.

Rahoton da ya gabatar wa Akawun Majalisar a watan Agusta ya ce,  an kashe kudaden ne a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2018 ba tare da cike takardun da suka dace ko rasitin kayan da a ka saya ba.

A shekarar da ta gabata ne kwamitin kudaden gwamnati na majalisar ya kaddamar da bincike kan hukumomi da ma’aikatun gwamnatin tarayya daga 2015 zuwa 2018.

A watan Yunin bana ne kwamitin da rahoton binciken wata shidan da ya gudanar a kan hukumomin.

Da ya ke bayani kan lamarin, shugaban cibiyar bin diddigi da tabbatar da gaskiya a harkokin majalisa (CISLAC), Auwal Musa Rafsanjani, ya ce wannan abin takaici ne kamar yadda Aminiya ta rawaito.

Sai dai a martaninsa, Akawun Majalisar Tarayya, Austen Adesoro, ya ce abubuwan da ake batu sun shafi shekarar 2019 kuma tuni a ka shawo kansu.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuÆ™uru wajen daÆ™ile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta É—auki É—an wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen É—an wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe Æ´an Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp