Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya ce gwamnatin jihar Kano za ta horas da matasa aikin noma ta hanyar amfani da na’urorin zamani, domin inganta noma da kiwo a fadin jihar baki daya.
Ganduje na bayyana hakan ne a lokacin da gwamnatin tarayya ta shirya samar da masanaantar kyankyasar Kaji a jihar Kano, domin bunkasa kiwon kaji a wani bangare na kara bunkasa tattalin arziki.
Ministan kimiya, fasaha da kirkire-kirkire, Dr Ogbannaya Onu ne ya sanar da hakan a yayin da ya kawo ziyara gwajen gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
Dr .Ogbonnaya Onu, ya ce“Gwamnatin tarayya za ta baiwa matasa horo na musamman a kan ilimin fasaha da sarrafa kayan amfanin gona da nufin rage zaman kashe wando a tsakanin matasa”.