fidelitybank

KDC ta fara wayar da kan malaman Tsangayu a Kano

Date:

Wata Kungiya mai zaman kanta da ke fafutukar kawo sauyi ga tsarin Ilimi na Almajiri, KDC Foundation, ta dauki nauyin malaman Makarantun Tsangaya, domin tattaunawa da wayar da kan su kan sabon manhajar da ta tsara na tafiyar da makarantun Tsangaya.

Tattaunawar wadda ta gudana a ranar Litinin a Kano, tare da masu ruwa da tsaki daga gwamnatin tarayya da na jiha da malaman makarantu da kafafen yada labarai wanda ya ta ta’allaka ne kan hanyoyin zaburar da malaman Islamiyya, domin su amince da sauye-sauye masu kyau daga manhajar karatu.

Solacebase ta rawaito cewa, shugaban gidauniyar, Khalifa Muhammad Dankadai, ya ce, makasudin taron shi ne domin jin ta bakin malaman Islamiyya kan yadda suke kallon manhajar da kuma samun abubuwan da suka dace, domin tsara yadda ya dace da ra’ayinsu.

Ya ce “Ta hanyar nazarin abubuwan da malaman Islamiyya suka bayar, an tabbatar da cewa sun amince da tsarin kuma a shirye suke su yi aiki da shi a duk lokacin da aka samu wanda shi ne babban damuwarmu. Domin dole ne su yarda kuma su yi aiki tare da tsarin karatun sannan za mu cimma burinmu na gyara tsarin.

“Don haka za mu yi la’akari da ra’ayoyinsu tare da ba su hannu ‘yanci, domin gudanar da tsarin da kansu. Daga cikin abin da za mu yi shi ne koyar da Turanci da Lissafi, da kuma koyar da yara kanana sana’o’in kasuwanci ta yadda za su daina barace-barace a kan tituna da kuma yin ado da kyau kamar sauran daliban,” inji shi.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp